Wwwauwalalhassancomng

Wwwauwalalhassancomng Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Wwwauwalalhassancomng, Advertising/Marketing, 43 number 13, Kaduna.

*** Yaran Muhammad buhari kenan da yahaifa arayuwarsa Marubuci daga✍️✍️ Auwal y Alhassan
15/07/2025

*** Yaran Muhammad buhari kenan da yahaifa arayuwarsa

Marubuci daga✍️✍️ Auwal y Alhassan

23/01/2021
LABARI DA DUMI DUMINSA FROM AY ALHASSAN
23/09/2019

LABARI DA DUMI DUMINSA FROM AY ALHASSAN

23/09/2019

Da duminsa: Allah ya jarabci babban limamin Masallacin Madina, Sheikh Ali Al Hudaify, da bugun jini.

An garzaya fa shi Asibiti.

Allah ya Kara masa lafiya.

23/09/2019
23/09/2019

GWAMNA GANDUJE YA AMINCE DA NAƊIN MEMBOBIN HUKUMAR TALLAFAWA HARKOKIN KIWON LAFIYAR AL'UMMAR JIHAR KANO

DAGA Bashir Abdullahi El-bash

-Kafin Mu Ba Su Waɗannan Muƙamai, Sai Da Mu Ka Yi Nazari Game Da Tarihin Ayyukansu Na Baya - Gwamna Ganduje.

-Mun Kafa Wannan Hukuma Ne Kan Manufar Yi Wa Al'umma Aiki Da Kuma Tallafa Musu Gami Da Ciyar Da Fannin Lafiya Gaba, Ina Fatan Za Ku Kiyaye Da Wannan - Gwamna Ganduje.

Yau Lahadi, 22 ga watan Satumba, 2019.
Mai girma gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, a wannan rana ya amince da naɗin membobin hukumar da aka kafa domin ta jiɓinci lamarin haɗa gudunmawar tallafawa harkokin kula da tsarin kiwon lafiya a Jihar Kano, wato" Kano State Contributory Healthcare Management Agency", waɗanda kuma naɗin nasu ya fara aiki ne nan take.

Daga cikin membobin hukumar, gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya amince da naɗin Dakta Bashir Muhammad Ɗankadai, a matsayin shugaban hukumar, ya yin kuma da ya amince da naɗin Dakta Halima Muhammad Mijinyawa, a matsayin sakatariyar hukumar ta (Kano State Contributory Healthcare Management Agency).

Sauran membobin hukumar sun haɗa da:

(1). Halima Musa Yakasai, wakiliya daga ma'aikatar lafiya ta Jihar Kano, wato (State Ministry Of Health).

(2). Musa Namadi Karefa (Daraktan albashi), wakili daga ofishin shugaban ma'aikata na Jiha, (Head Of Service).

(3). Tayyib Na'abba, (Daraktan kasafin kuɗi), wakili daga ma'aikatar tsare-tsare da kasafin kuɗi ta jihar Kano, wato (State Ministry Of Budget And Planning).

(4). Hafsat Kolo, wakiliya daga ƙungiyoyi masu zaman kansu, wato "Civil Society Organisations" (CSOs).

(5). Muhammad Isyaku Yammedi, wakili daga hukumar inshorar lafiya ta ƙasa, "National Health Insurance Scheme" (NHIS).

(6). Dakta Maryam Muhammad Suleiman wakiliya daga ƙungiyar likitoci ta ƙasa, (NMA).

(7). Hadiza Salisu Rogo da kuma Yakubu Abdullahi Esq, su ne wakilai daga ƙungiyar majalissar ƙolin haɗakar ƙungiyoyin ma'aikata na tarayya.

(8). Sai kuma sauran membobin hukumar waɗanda su ka wakilci ƙungiyar ƴan ƙwadago ta ƙasa, (NLC) da waɗanda su ka wakilci haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƴan kasuwa ta ƙasa, (TUC).

Sannan kuma, akwai sauran membobin hukumar waɗanda ba a faɗa ba a yanzu, su ma nan gaba za a gabatar da sunayensu da kuma ma'aikata ko hukumomin da su ka fito.

A ya yin da ya ke taya su murna, gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya buƙaci duk waɗanda ya ba wa wannan muƙamai da su kiyaye da muradin da aka gina wannan hukuma akai na kawo gyara da samar da ingantaccen cigaba a fannin lafiya.

"Ina amfani da wannan dama wajen jan hankalinku da tunasar da ku cewa wannan tsari ya na da matuƙar tasiri ga Jiharmu, an kafa wannan hukuma ne kan doka da manufar yi wa al'umma aiki da tallafa musu, sannan duk waɗanda mu ka ba wa waɗannan muƙamai mun yi duba da tarihin ayyukansu na baya, mu na sa ran za su yi aiki cikin nagarta da amince tare da la'akari da sauye-sauyen zamani kamar yadda Duniya ta ke tafe a yau". Inji Gwamna Ganduje.

23/09/2019

Zan fito takarar shugaban kasa 2023 – Dan majalisa Gudaji Kazaure

Dan majalisar daga jahar Jigawa , dake wakiltar mazabar Roni, Kazaure da Yan kwashi, Honorabul Muhammad Gudaji Kazaure ya bayyana cewa mukamin dan majalisa ta mai kadan, don haka takarar shugaban kasa ce a gabansa.

Gudaji ya bayyana haka ne yayin da yake ganawa da gidan rediyon BBC Hausa, inda aka tambayeshi game da abin da yake ciki bayan bai samu nasara a kokarinsa na tsayawa takarar shugabancin majalisar wakilai ba.

Amma Gudaji ya amsa cewa tun bayan da jam’iyyar APC ta bashi hakuri game da takarar kujerar kaakakin majalisar wakilai, shi ma ya hakura.

“Na fidda rai, amma idan Allah Yasa an sake dawowa, toh sai inda karfina ya kare.”

Gudaji ya kara da cewa yana da burin tsayawa takarar shugaban kasar Najeriya ko kuma takarar gwamnan jahar Jigawa domin ya samu daman taimaka ma talaka yadda ya kamata, saboda a cewarsa taimakon da yake yi ma talaka a kujerar dan majalisa ta yi kadan.

“Idan kuma na samu cigaba, yadda nake so shi ne takarar shugaban kasa ko kuma takarar gwamna, dan majalisar ma ni gani nake yi bana iya talaka wani abu sosai, amma can inda za’a kawo kayan talakawa, toh can ne nake ganin zan iya kaisu inda talaka zai amfana.

“Duk abinda gwamnati ta kawo da muke ganin zai iya ma talaka illa, indai muna nan zamu ce a’a, kana gani kwanan nan da babban banki s**a kafa dokar ajiyar kudi cewar idan an kai ajiyan kudi za’a dinga cire wani abu muka mike muka ce bamu yarda ba.” Inji shi.

23/09/2019

A corps member named Igwebuike Amilia Nkechi with registration number PL/19B/1423 was abducted from her home in Jos in the early hours of Monday morning by suspected kidnappers.

23/09/2019

The body of the Commandant of the Armed Forces Command and Staff College Secondary School, Jaji in Kaduna State, O.O. Ogundana has been found in a shallow well near the Deeper life Church in Jaji Cantonment. The deceased, a commodore in the Nigerian Navy based in Jaji, Kaduna State, was said to have...

Address

43 Number 13
Kaduna
KARKABARIKANKATAKULLE

Telephone

08179680456

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Wwwauwalalhassancomng posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share