08/07/2022
MUDI DA MATARSA
Mudi ya ce wa matarsa, "idan mun sami ruwa gobe, zan tafi gona aiki, idan kuma ba a yi ruwa ba, zan yi gyaran kwatamin can na ƙofar gida, da yake damun mu da ɗoyi.'"
Matar ta ce, "Maigida, ba ka ce insha Allahu ba."
Sai kuwa ya hau ta da faɗa, "To Sayyada! Ko na ce insha Allahu ko ban ce ba, dole cikin biyun nan gobe a yi ɗaya. Ko dai na tafi gona ko na yi aiki a ƙofar gida."
Allah da ikonsa, sai gari ya tashi tangaram. Mudi ya saɓi magirbi ya nufi ƙofar gida wajen gyaran kwata. Yana kunno kai waje, sai kwalawa s**a yi ram da shi. Ashe su kuma sun biyo wani mai laifi ne, da ya zo daidai zauren gidan Mudi, sai ya yi kamar ciki ya afka, ashe arcewa ya yi ba su lura ba. Tun a cikin mota s**a fara ƙera shi.
Mudi ya sha gwale-gwale sosai a caji ofis, har sai da ya fita hayyacinsa. Daga ƙarshe 'yansanda s**a gane ba mutumin da suke nema ba ne. S**a ba shi haƙuri, s**a sallame shi. Da ya dawo gida, sai ya ƙwanƙwasa ƙofa. Matar ta ce, "waye?"
Ya ce, "Mudi ne, insha Allah!"
Bukar Mada
08/07/2022