18/03/2026
Wallahi a yanzu dai, idan ka cire burin gamawa da duniya lafiya da nake yi, na rantse da Allah, ba ni da wani buri a duniya da ya fi in ga Afirka da ƙasata Najeriya sun gyaru. Ina matuƙar son yankin nan wallahi.
Babu abin da yake ba ni takaici irin in ga duk wani yanki a duniya yana ci gaba amma ban da namu. Babu ilimi, babu lafiya, babu ruwa, babu wuta, babu hanyoyi, babu kimiyya da fasahohi, babu tsaro, babu ƴancin ɗan’adam, babu masana’antu — babu komai! Wai shin mu ba za mu rayu k**ar sauran sassan duniya ba? Wannan wacce irin nahiya ce da za mu yi ta rayuwa k**ar waɗanda babu ƙwaƙwale a cikin kawunansu?
Kullum muna cewa shugabanni da Turawa na zaluntar mu amma mafi yawa daga cikin al’ummarmu duk mun zama azzalumai. Kowa kansa yake so bai damu da wani ba. Kowa duniya yake nema ta kowanne hali bai damu da lahira ba. Kowa tsaro da kariyar kansa yake nema amma bai damu da halin da wasu suke ciki ba. Anya mu mutane ne ma kuwa? Yanzu a haka za mu ci gaba da rayuwa? A haka ƴaƴanmu za su zo su yi kyakkyawar rayuwa gobe? Wannan ita ce goben da muke gina musu?
Me ya sa ba za mu cire son zuciya mu fara samar da gyara daga kanmu ba? Me ya sa mu ma ba za mu zama masu adalci ga kawunanmu ba? A ce babu mai gaskiya da amfani sai wanda yake da alaƙa da kai, kuma babu mara gaskiya, mai cutarwa sai wanda ba shi da alaƙa da kai?
Gwamnati ba ta hukunta masu laifi sai waɗanda ba sa tare da ita, shi ma talaka ba ya son a faɗi laifin ɗan’uwansa sai dai na wani. Shi ya sa su ma shugabannin ba sa ma batun kawo gyara saboda dama daga cikinmu suke kuma irin halayenmu ne da su, kuma sun ga har yau ba mu shirya ba.
Imu-imu talakawa rayuwa muke yi kara zube; babu adalci, babu gaskiya, babu amana da alƙawari. Kowa ya samu dama sai ya zalunci ɗan’uwansa da uzurin cewa wai ai kowa ma idan ya samu dama wai haka zai yi. Anya wannan nahiyar tamu za ta gyaru kuwa? Yanzu da wannan tunanin muke tunanin samun canji? Waye zai fara gyarawa daga cikinmu kenan?
Wallahi ba fata nake yi ba, amma ko ɗana ne da na haifa yake aikata wani mummunan aiki sai na sallama shi ga hukuma ko in barranta da shi. Shi ya sa sam ba zan iya siyasa ba. Don wataƙila azzalumai ne za su kashe ni akan al’ummar da ba ta san yaƙin da kake yi mata ba.
Shi ya sa a wurin aikina ma ni ban sami faada ba, saboda ni ba na ganin rashin daidai ban yi magana ba.
Allah ya ganar da al’ummarmu!
⚖️