15/07/2026
'Yar takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar karamar hukumar Ungogo ta bayyana aniyarta ta tsayawa takara domin wakiltar al'ummar karamar hukumarta tare da bayar da gudunmawa wajen samar da dokoki da manufofin da za su inganta rayuwar jama'a.
A cewarta, babban burinta shi ne kare muradun al'ummar karamar hukumar a Majalisar Dokokin Jihar Kano, tare da tabbatar da an gudanar da ayyukan ci gaba cikin adalci da gaskiya. Ta kuma yi alƙawarin yin aiki kafaɗa da kafaɗa da al'umma domin magance matsalolin da s**a shafi ilimi, lafiya, matasa, mata, samar da ayyukan yi, da bunƙasa ababen more rayuwa.
Ta yi kira ga al'ummar karamar hukumar da su ci gaba da ba ta goyon baya da haɗin kai domin cimma manufofin ci gaba da walwalar kowa da kowa.