Sen. Muntari Dandutse Media Reporters

Sen. Muntari Dandutse Media Reporters Chairman Senate Committee on Tertiary
Institutions and TetFund | Senator
representing Katsina South Senatorial
District, Katsina State.

PRESS RELEASE..The Senator representing Katsina South and Chairman of the Senate Committee on Tertiary Education and TET...
29/04/2026

PRESS RELEASE..

The Senator representing Katsina South and Chairman of the Senate Committee on Tertiary Education and TETFund, Senator Muntari Mohammed Dandutse, has expressed his appreciation to the Governor of Katsina State, Malam Dikko Umaru Radda, PHD, for his exemplary leadership, wisdom, and foresight in fostering peace and unity within the All Progressives Congress (APC), particularly during the consensus process for the party’s primary elections.

In a statement he issued, the Senator commended the contributions of party leaders, elders, stakeholders, and committees involved in planning and implementing the process, noting that it was conducted peacefully, fairly, and with a strong sense of party loyalty.

Senator Dandutse described the consensus arrangement as a sign of political maturity, emphasizing the importance of prioritizing unity over differences in order to achieve future success.

Regarding aspirants who were not successful, the Senator urged them to accept the outcome with patience and resilience, and to view it as part of the democratic process. He added that the party is proud of their contributions, dedication, and sacrifices, and that opportunities for continued service remain open to them.

He also called on party supporters and the general public to remain calm, avoid actions that could lead to division, and continue supporting leadership to ensure sustained peace and development.

Senator Dandutse further emphasized the importance of forgiveness, tolerance, and unity at this time, noting that the success of the party is a collective achievement, and that unity remains the foundation for victory in the forthcoming general elections.

In conclusion, he prayed for an end to all forms of unrest across the country, for lasting peace, for unity among the people, and that all efforts made will yield positive outcomes for the people of Katsina State and Nigeria as a whole.

Signed:
Senator Muntari Mohammed Dandutse, Chairman, Senate Committee on Tertiary Education and TETFund

Bismillahir Rahmanir RahimKatsina APC Consensus UpdateAn Cimma Matsaya Kan Takarar Sanata a Yankin FuntuaBayan wani muhi...
28/04/2026

Bismillahir Rahmanir Rahim

Katsina APC Consensus Update

An Cimma Matsaya Kan Takarar Sanata a Yankin Funtua

Bayan wani muhimmin zama da aka gudanar tsakanin manyan masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar APC daga yankin Funtua tare da Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, an cimma matsaya kan takarar Sanata a yankin.

A sakamakon zaman, an amince da Sanata Muntari Mohammed Dandutse a matsayin ɗan takarar Sanata na yankin Funtua ta hanyar tsarin sasanci (consensus).

Haka kuma, Hon. Hamza Sule Faskari ya samu tikitin tsayawa takarar ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Faskari/Sabuwa/Kankara.

Wannan matsaya na nuni da cikakken haɗin kai da fahimtar juna tsakanin shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar, domin dinke baraka, ƙarfafa zumunci, da kuma shirya APC yadda ya kamata domin samun nasara a zaɓen shekarar 2027.

28/04/2026

Sako na musamman ga Al'umma karaduwa Daga Maigirma sanata muntari Dandutse

Sanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya halarci taron masu ruwa da tsaki ...
26/04/2026

Sanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya halarci taron masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar APC da aka gudanar a yau Lahadi a birnin Katsina.

A yayin taron, jam’iyyar ta amince da amfani da tsarin sasanci/sulhu (consensus) wajen gudanar da zaɓen fidda gwani na kakar zaɓen shekarar 2027.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin jam’iyya da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar.

Da yake jawabi, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira ga mambobin jam’iyyar da su rungumi haɗin kai, ladabi da kuma sauke amanar da al’umma ta ɗora musu, yayin da jam’iyyar ke shirin tunkarar zaɓukan da ke tafe.

Gwamnan ya jaddada muhimmancin ci gaba da hulɗa da ‘ya’yan jam’iyya da al’umma domin ƙarfafa dimokuraɗiyya da ginshikin APC a jihar.

Ya bayyana cewa an yi la’akari da tsarin sulhu ne bayan tattaunawa da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, inda ya ce tsarin zai ba da damar yin sasanci inda ya dace, tare da gudanar da zaɓe a wuraren da hakan ya zama dole.

A cewarsa, tsarin sulhu zai taimaka wajen rage rikice-rikicen cikin gida, ƙarfafa haɗin kai, da kuma inganta zaman lafiya a cikin jam’iyya.

Gwamna Radda ya kuma gargaɗi masu neman takara da su guji kashe kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba, yana mai cewa shugabanci nauyi ne da ya kamata a ɗauka da gaskiya, rikon amana da tawali’u.

Hakazalika, ya buƙaci mambobin jam’iyyar da su fifita muradun jam’iyya fiye da na kansu, tare da mara wa waɗanda s**a samu nasara baya domin ciyar da jam’iyyar gaba.

A nasa jawabin, Shugaban APC na Jihar Katsina, Alhaji Bashir Gambo Saulawa, ya yaba wa masu ruwa da tsaki bisa goyon bayan da suke bai wa jam’iyyar, tare da jaddada shirinta na gudanar da zaɓen fidda gwani cikin nasara.

Ya sanar da cewa an fitar da jadawalin zaɓen fidda gwani domin ba da cikakken jagoranci ga dukkan matakan da s**a shafi gudanar da zaɓukan.

Saulawa ya ce jam’iyyar za ta yi amfani da tsarin sulhu inda ya dace, biyo bayan shawarwari masu zurfi da masu ruwa da tsaki, domin ƙarfafa haɗin kai da rage rikice-rikice.

Haka kuma, ya sanar da kafa muhimman kwamitoci da s**a haɗa da Kwamitin Sulhu da Sasanci wanda tsohon gwamna Aminu Bello Masari ke jagoranta, tare da tsohon gwamna Ibrahim Shehu Shema a matsayin mataimaki.

An kuma kafa kwamitocin sulhu na yankuna uku: Katsina (Sanata Ibrahim Ida), Funtua (Hon. Tukur Ahmed Jikamshi) da Daura (Arc. Ahmed Musa Dangiwa).

Bugu da ƙari, an kafa Kwamitin Tabbatarwa (Affirmation Committee) domin tabbatar da gaskiya da adalci a dukkan matakan zaɓen.

Taron ya samu halartar mataimakin gwamna, shugaban majalisar dokokin jiha, mambobin majalisun dokoki na ƙasa da jiha, da wakilai daga ƙananan hukumomi 34 na jihar.

Jam’iyyar APC ta nuna ƙwarin gwiwa cewa tsarin sulhu zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai da kuma samun nasara a zaɓukan 2027.

Dandutse Media Reporter
Sanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya halarci taron masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar APC da aka gudanar a yau Lahadi a birnin Katsina.

A yayin taron, jam’iyyar ta amince da amfani da tsarin sasanci/sulhu (consensus) wajen gudanar da zaɓen fidda gwani na kakar zaɓen shekarar 2027.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin jam’iyya da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar.

Da yake jawabi, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira ga mambobin jam’iyyar da su rungumi haɗin kai, ladabi da kuma sauke amanar da al’umma ta ɗora musu, yayin da jam’iyyar ke shirin tunkarar zaɓukan da ke tafe.

Gwamnan ya jaddada muhimmancin ci gaba da hulɗa da ‘ya’yan jam’iyya da al’umma domin ƙarfafa dimokuraɗiyya da ginshikin APC a jihar.

Ya bayyana cewa an yi la’akari da tsarin sulhu ne bayan tattaunawa da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, inda ya ce tsarin zai ba da damar yin sasanci inda ya dace, tare da gudanar da zaɓe a wuraren da hakan ya zama dole.

A cewarsa, tsarin sulhu zai taimaka wajen rage rikice-rikicen cikin gida, ƙarfafa haɗin kai, da kuma inganta zaman lafiya a cikin jam’iyya.

Gwamna Radda ya kuma gargaɗi masu neman takara da su guji kashe kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba, yana mai cewa shugabanci nauyi ne da ya kamata a ɗauka da gaskiya, rikon amana da tawali’u.

Hakazalika, ya buƙaci mambobin jam’iyyar da su fifita muradun jam’iyya fiye da na kansu, tare da mara wa waɗanda s**a samu nasara baya domin ciyar da jam’iyyar gaba.

A nasa jawabin, Shugaban APC na Jihar Katsina, Alhaji Bashir Gambo Saulawa, ya yaba wa masu ruwa da tsaki bisa goyon bayan da suke bai wa jam’iyyar, tare da jaddada shirinta na gudanar da zaɓen fidda gwani cikin nasara.

Ya sanar da cewa an fitar da jadawalin zaɓen fidda gwani domin ba da cikakken jagoranci ga dukkan matakan da s**a shafi gudanar da zaɓukan.

Saulawa ya ce jam’iyyar za ta yi amfani da tsarin sulhu inda ya dace, biyo bayan shawarwari masu zurfi da masu ruwa da tsaki, domin ƙarfafa haɗin kai da rage rikice-rikice.

Haka kuma, ya sanar da kafa muhimman kwamitoci da s**a haɗa da Kwamitin Sulhu da Sasanci wanda tsohon gwamna Aminu Bello Masari ke jagoranta, tare da tsohon gwamna Ibrahim Shehu Shema a matsayin mataimaki.

An kuma kafa kwamitocin sulhu na yankuna uku: Katsina (Sanata Ibrahim Ida), Funtua (Hon. Tukur Ahmed Jikamshi) da Daura (Arc. Ahmed Musa Dangiwa).

Bugu da ƙari, an kafa Kwamitin Tabbatarwa (Affirmation Committee) domin tabbatar da gaskiya da adalci a dukkan matakan zaɓen.

Taron ya samu halartar mataimakin gwamna, shugaban majalisar dokokin jiha, mambobin majalisun dokoki na ƙasa da jiha, da wakilai daga ƙananan hukumomi 34 na jihar.

Jam’iyyar APC ta nuna ƙwarin gwiwa cewa tsarin sulhu zai taimaka wajen ƙarfafa haɗin kai da kuma samun nasara a zaɓukan 2027.

Dandutse Media Reporter
26 ga Afrilu, 2026
26 ga Afrilu, 2026

Allahumma in kana hadhal amru khairan li Abdika Maigirma Sanata Muntari Mohammed Dandutse fi dinihi wa ma’ashihi wa ‘aqi...
26/04/2026

Allahumma in kana hadhal amru khairan li Abdika Maigirma Sanata Muntari Mohammed Dandutse fi dinihi wa ma’ashihi wa ‘aqibati amrihi faqdurhu lahu wa yassirhu lahu, thumma barik lahu fihi. Wa in kana sharran lahu fasrifhu ‘anhu wasrifhu ‘anhu, waqdur lahu al-khaira haithu kana thumma ardhihi.”

Sanata Dandutse ya halarci daurin auren ɗansa Sadik tujjani Dandutse a FuntuaFitaccen ɗan majalisar dattawa mai wakiltar...
25/04/2026

Sanata Dandutse ya halarci daurin auren ɗansa Sadik tujjani Dandutse a Funtua

Fitaccen ɗan majalisar dattawa mai wakiltar Katsina ta Kudu, Sanata Muntari Mohammed Dandutse, ya halarci daurin auren ɗansa, Sadiq Tijjani Dandutse, da amaryarsa Asma’u Sani Maijama’a a garin Funtua.

An gudanar da bikin ne a ranar Juma’a, 24 ga watan Afrilu, 2026, a Masallacin Juma’a na Kasuwar Mata da ke kan titin Sokoto Bye-Pass a Funtua, kamar yadda ke kunshe a cikin katin gayyatar auren.

Sanata Dandutse shi ne ya kasance waliyyin ango, inda ya karɓi auren Sadik tujjani Dandutse Dan yayanshi Alhaji Tujjani Dandutse Funtua.

Bikin ya samu halartar manyan baƙi daga sassa daban-daban, ciki har da wasu jami’an gwamnati da ‘yan siyasa. Daga cikin waɗanda s**a halarta akwai Hon. Musa Adamu Funtua Kwamishinan lafiya na jihar Katsina da Hon. Ibrahim Sha’abu, mai neman tsayawa takarar kujerar Funtua/ Dandume.

Haka kuma, Hakimin Funtua, Mai Martaba HRH Sambo Idris Sambo, ya halarci bikin tare da sauran al’umma domin shaida wannan muhimmin taro na farin ciki.

An gudanar da daurin auren cikin nasara da kwanciyar hankali, inda mahalarta s**a taya iyalan amarya da ango murna tare da yi musu fatan alheri da zaman lafiya a rayuwar auratayya.

Dandutse Media Reporter

Waliyyin Siyasa, Gwarzon Al’umma – Sanata Muntari Muhammad DandutseIdan ana magana a kan shugabanci, ana nufin riƙon ama...
23/04/2026

Waliyyin Siyasa, Gwarzon Al’umma – Sanata Muntari Muhammad Dandutse

Idan ana magana a kan shugabanci, ana nufin riƙon amana ne. Idan ana magana a kan jagoranci, ana nufin gaskiya da adalci. Idan kuma ana neman fitila da za ta haskaka duhun siyasar Katsina ta Kudu, da ma jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya, babu shakka sunan da zai fara bayyana shi ne na Sanata Muntari Muhammad Dandutse.

Sanata Dandutse ba kawai ɗan siyasa ba ne; waliyyin al’umma ne, jagoran gaskiya, kuma garkuwa ga talakawa. Ya ɗauki buƙatun matasa a matsayin nasa, ya ɗauki ci gaban al’umma a matsayin nauyin da Allah Ya ɗora masa.

Mutakka Babangida daga Faskari na daga cikin waɗanda wannan jagora ya taimaka musu wajen samun aiki. Shi da kansa ya bayyana cewa shi da abokansa sun amfana da mukaman gwamnati daga Sanata Dandutse ba tare da wani sharadi ba, ba tare da neman yabo ko ɗaukar hoto a kafafen sada zumunta ba. Wannan hali ne na shugaba nagari—wanda ke son ganin matasa sun ci gaba, sun zama nagartattun mutane, ba wai masu yi masa kirari kawai ba.

A wannan zamani da siyasa ta zama hanyar farfaganda da neman suna, Sanata Dandutse ya bambanta. A wurinsa, siyasa hidima ce kuma ibada ce—hanya ce ta kyautata rayuwar al’umma. Wannan ne ya sa matasa da dama a Funtua Zone s**a samu ayyukan yi a matakai daban-daban na gwamnati; wasu a rundunar ’yan sanda, wasu a ma’aikatun tarayya, wasu kuma a shirye-shiryen dogaro da kai.

Sanata Muntari Dandutse ya zama tushen bege ga matasa, garkuwa ga talakawa, kuma madubi ga sauran ’yan siyasa. Irin wannan shugabanci ba wai mulki kawai ba ne, tarihi ne mai daraja wanda ba zai goge ba.

Hakika, wannan shi ne gwarzon al’umma—jagoran gaskiya, shugaba nagari wanda ya kafa tarihi na adalci, riƙon amana da kyakkyawan jagoranci da ya kamata kowa ya yi koyi da shi.

Saboda haka, muna kira ga al’ummar Katsina ta Kudu da su ƙara bai wa Sanata Muntari Muhammad Dandutse dama domin ci gaba da ayyukan alheri.

Sanata Muntari Dandutse Media Reporter

Maigirma Sanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya karɓi baƙuncin Hon. Sagi...
22/04/2026

Maigirma Sanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya karɓi baƙuncin Hon. Sagir Lawal Dan Sango, tsohon Sakataren Ƙaramar Hukumar Funtua, a ofishinsa da ke Abuja.

Ziyarar wadda ta kasance ta sada zumunci, ta bai wa ɓangarorin biyu damar tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi cigaban Ƙaramar Hukumar Funtua da ma yankin baki ɗaya.

A yayin ganawar, an mayar da hankali kan hanyoyin inganta walwala da ci gaban al’umma, tare da ƙarfafa haɗin kai da haɗin gwiwa tsakanin shugabanni da al’umma domin tabbatar da dorewar cigaba.

Sanata Dandutse ya jaddada kudurinsa na ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen raya ƙasa, musamman waɗanda za su amfani al’ummar mazabarsa.

Dandutse Media Reporter

Al'ummar Shiyyar karaduwa sun amince da Sanata Muntari Dandutse Mohammed A Karo Na BiyuDaga: Shamsu Wapa DandumeZama a s...
21/04/2026

Al'ummar Shiyyar karaduwa sun amince da Sanata Muntari Dandutse Mohammed A Karo Na Biyu

Daga: Shamsu Wapa Dandume

Zama a sahun gaba na siyasa tsawon sama da shekaru ashirin da biyar ba ƙaramin abu ba ne, Musamman a ƙasa irin tamu inda gwagwarmaya, juriya da kuma ƙwarewar shugabanci suke zama ginshiƙai na nasara.

Ga Sanata Muntari Mohammed Dandutse, wannan tafiya ba kawai ta ƙara masa kwarewa ba ce, har ma ta bayyana irin ƙalubalen da ke tattare da zama jagora, Inda nasara ke haifar da yabo, amma kuma tana jawo hassada da adawa daga wasu ɓangarori.

Tun daga matakin kantoma na riƙo, zuwa zaɓaɓɓen ɗan majalisar wakilai, har zuwa matsayin sanata mai wakiltar shiyyar Funtua, Dandutse ya gina tarihin siyasa mai cike da jajircewa da sadaukarwa. Wannan tsari na ci gaba a matakai daban-daban na shugabanci ya nuna gogewarsa da kuma yadda ya samu amincewar jama’a a tsawon lokaci.

Sai dai kamar yadda aka saba a harkar siyasa, samun irin wannan matsayi na jawo masu s**a, wasu bisa hujja, wasu kuma bisa son rai. Amma tambayar ita ce:

*Shin ya kamata a yanke hukunci bisa jita-jita da surutun ‘yan siyasa marasa alkibla, ko kuma a duba tarihi da ayyukan da aka gani da ido?

A siyasance, al’umma ce ginshiƙi bawai muradin mutum ɗaya ko ƙungiya ba, Don haka, yana da muhimmanci masu zabe su yi nazari mai zurfi kan tarihin shugabanni, su auna su bisa ayyuka da tasirin da s**a yi, ba wai bisa hayaniyar masu anfani da siyasa domin biyan bukatunsu ba.

Tarihin Sanata Muntari Mohammed Dandutse ya nuna shi a matsayin jagora mai riƙon amana, mai gaskiya da fahimtar yadda ake tafiyar da al’umma. Wannan ne ya sa al’ummar yankin Karaduwa s**a sake nuna masa amincewa domin ya ci gaba da jagoranci a karo na gaba, duk da ƙoƙarin wasu masu neman tayar da ƙura domin cimma muradunsu.

A ƙarshe, darasi a nan shi ne: .

*Siyasa ba ta yaudara ba ce, kuma tarihi ba ya ɓoye gaskiya. Duk wanda ke son jagoranci, dole ne ya kasance a shirye ya fuskanci duka yabo da s**a, amma abin da ya fi muhimmanci shi ne abin da ya bari a zuciyar al’umma.

Al'ummar Shiyyar karaduwa sun amince da Sanata Muntari Dandutse Mohammed A Karo Na Biyu

Sunayen Wasu Daga Cikin Wadanda Sanata Muntari Mohammed Dandutse Ya Samar Wa Aikin yi a matakai Daban daban Daga cikin w...
21/04/2026

Sunayen Wasu Daga Cikin Wadanda Sanata Muntari Mohammed Dandutse Ya Samar Wa Aikin yi a matakai Daban daban

Daga cikin wadanda s**a samu wannan dama akwai:

1. Adamu Abubakar Sadiq

2. Mustapha Abdulrashid

3. Usman Ibrahim

4. Kabir Abdul Wahab

5. Kamal Badamasi Labbo

6. Yakuba Umar Isah

7. Usman Mu’azu

Wadannan matasa na daga cikin wadanda aka bai wa damar shiga sabbin matakan rayuwa ta fuskar aiki, wanda ake sa ran zai taimaka wajen inganta rayuwarsu da ta iyalansu.

A karshe, ana addu’ar Allah Ya sanya albarka a wannan aiki, Ya kuma ba su nasara da daukaka a sabuwar matakin da s**a shiga.

Hakazalika, ana fatan Allah Ya saka wa Sanata Muntari Mohammed Dandutse da alheri bisa wannan gudunmawa ga al’umma.

Sanata Muntari Mohammed Dandutse ya karɓi baƙuncin Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina, Hon. Musa Adamu Funtua, a ofishi...
20/04/2026

Sanata Muntari Mohammed Dandutse ya karɓi baƙuncin Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina, Hon. Musa Adamu Funtua, a ofishinsa da ke Abuja.

Ziyarar wacce ta kasance ta sada zumunci ta ba su damar tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi ci gaban al’umma

Kwamishinan ya samu rakiyar Hon. Imam Ibrahim Danmummuni, Wanban Katukan Katsina kuma Galadiman Scrap.

Dandutse Media Reporter

PRESS RELEASESenator Muntari Dandutse Celebrates Aide on His BirthdayThe Senator representing Katsina South Senatorial D...
19/04/2026

PRESS RELEASE

Senator Muntari Dandutse Celebrates Aide on His Birthday

The Senator representing Katsina South Senatorial District, Muntari Mohammed Dandutse, has extended warm birthday wishes to his aide, Malam Abubakar Nuhu Ahmad (Ƙarfi), on the occasion of his birthday anniversary.

In a statement issued by the Senator, he described Malam Abubakar as a dedicated, dependable, and trustworthy individual who plays a significant role in his capacity as a Senior Legislative Aide.

Senator Dandutse commended his contributions to the effective running of the office and his commitment to public service.

He further wished him many more years in good health, continued success, and lasting progress in all his endeavors.

Happy Birthday 🎂

Dandutse Media Reporter

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sen. Muntari Dandutse Media Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share