ADC Safana

ADC Safana Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ADC Safana, Advertising/Marketing, Barhim, Katsina.

Da Dumi-DumiAPC ta fadi zaben gwamnan jihar OsunJam’iyyar APC ta shugaban Nijeriya Bola Tinubu ta sha kaye a zaben bayan...
16/08/2026

Da Dumi-Dumi

APC ta fadi zaben gwamnan jihar Osun

Jam’iyyar APC ta shugaban Nijeriya Bola Tinubu ta sha kaye a zaben bayan da INEC ta tabbatar da Gwamna Adeleke mai ci na jam’iyyar Accord a matsayin wanda ya lashe zaben.

Da ma dai jam’iyyar Accord ce ke mulkin jihar ta Osun, sai dai APC ta so karbe jihar daga hannun Accord party amma sakamakon zaben gwamnan jihar na 2026 da aka yi a ranar Asabar 15 ga watan Agusta ya nuna cewa Accord Party ta samu kuri’u 511,067 yayin da APC ta zo ta biyu da kuri’u 444,815 yayin da jam’iyyar ADC ta zo ta uku da kuri’u 17,180

"Hatta a cikin gidan Tinubu, ba Muslim-Muslim ake ba, Muslim-Christian ake yi, don haka babu dalilin Sheikh Sani Jingir ...
13/08/2026

"Hatta a cikin gidan Tinubu, ba Muslim-Muslim ake ba, Muslim-Christian ake yi, don haka babu dalilin Sheikh Sani Jingir na ci gaba da tallata takarar Tinubu".

--- Sanata Kwankwaso Dan takarar Mataimakin shugaban kasa a Jam'iyyar NDC.

Rabiu Musa Kwankwaso

Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Siyasa, ya yi kira ga al’ummar Jihar Katsina d...
13/08/2026

Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Siyasa, ya yi kira ga al’ummar Jihar Katsina da su mara wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu baya domin ya samu damar sake lashe zaɓen shugaban ƙasa a shekarar 2027.

Masari ya bayyana cewa sake zaɓen Shugaban Ƙasar a karo na biyu ya zama wajibi, yana mai cewa al’ummar Katsina na da alhakin mara wa gwamnatin Tinubu baya, musamman ganin yadda wasu ’yan jihar s**a samu muƙamai a gwamnatin tarayya.

Ya ce: “Ina kira ga al’ummar Jihar Katsina a taimaka Malam Bola Ahmed Tinubu ya sake zaɓe karo na biyu ya zama wajibi, saboda idan kun ga ba a yi muku daidai ba, mu ne da ya ba mu muƙamai.”

Alhaji Ibrahim Kabir Masari ya bayyana hakan ne yayin da yake magana kan siyasar ƙasar da kuma rawar da al’ummar Katsina za su taka a zaɓen 2027.

ADC Ta Yi Alkawarin  Takaita Kashe Kuɗin Gwamnati Idan Ta Lashe Zaɓen 2027Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta...
13/08/2026

ADC Ta Yi Alkawarin Takaita Kashe Kuɗin Gwamnati Idan Ta Lashe Zaɓen 2027

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta gabatar da wasu tsare-tsare masu faɗi kan yadda ya kamata a riƙa kashe kuɗaɗen gwamnati, ciki har da soke tsarin “Security Vote”, ƙara tsaurara matakan kula da tafiye-tafiyen jami’an gwamnati da kuma hana amfani da kadarorin gwamnati domin amfanin kashin kai, idan jam’iyyar ta kafa gwamnati a shekarar 2027.

Jam’iyyar ta ce waɗannan matakai wani ɓangare ne na babban shirin sake fasalin yadda ake gudanar da mulki a kasar, wanda aka tsara domin rage almubazzaranci, ƙarfafa bin diddigin yadda ake amfani da kuɗaɗen gwamnati da kuma mayar da albarkatun gwamnati wajen inganta rayuwar ’yan Najeriya da kuma ci gaban tattalin arziƙi.

An bayyana waɗannan tsare-tsare ne a cikin wani kundi me dauke da shafuka 25 na manufofin shugabanci da ƙa’idojin ɗabi’a na ADC, mai suna “The Orange Book”, wanda Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya ƙaddamar a Abuja ranar Talata.

Takardar ta mai da hankali sosai kan tsare-tsaren kashe kuɗi cikin hankali da kuma tabbatar da bin diddigin ayyukan hukumomin gwamnati, inda jam’iyyar ta ce dole ne gwamnati ta gudanar da harkokinta cikin ƙarin gaskiya da bayyananniyar hanya idan ana son Najeriya ta shawo kan matsalolin tattalin arziƙinta tare da dawo da amincewar jama’a.

Ɗaya daga cikin manyan shawarwarin jam’iyyar shi ne soke ware kuɗin “Security Vote” a matsayin kuɗi guda ɗaya da kuma sauran wasu kuɗaɗen tsaro da jam’iyyar ta ce ba sa samun cikakken bincike da sa ido daga majalisa.

A ƙarƙashin sabon tsarin da ADC ta gabatar, duk wani kuɗin da gwamnati za ta kashe wajen tsaro zai buƙaci sa ido, amincewa da kuma binciken majalisa, bisa tanade-tanaden dokokin ƙasa.

Jam’iyyar ta ce manufar wannan mataki ita ce rufe hanyoyin karkatar da kuɗaɗen gwamnati ko yin amfani da su ba bisa ka’ida ba, tare da tabbatar da cewa an yi amfani da kuɗaɗen da aka ware wa tsaro ne domin manufar da aka tanada mu

REGISTER. ORGANISE. LEAD. BEING AN ADDRESS BY HIS EXCELLENCY ATIKU ABUBAKAR, GCON, Waziri Adamawa, Vice President of Nig...
12/08/2026

REGISTER. ORGANISE. LEAD.

BEING AN ADDRESS BY HIS EXCELLENCY ATIKU ABUBAKAR, GCON, Waziri Adamawa, Vice President of Nigeria (1999–2007) and Presidential Candidate of the African Democratic Congress (ADC) AT THE NATIONAL YOUTH LEADERSHIP SUMMIT OF THE AFRICAN DEMOCRATIC CONGRESS
Abuja, Nigeria
12–13 August 2026

PROTOCOLS

I greet you in the unbreakable and unconquerable spirit of the African Democratic Congress!

Before I begin, let me ask the young people in this hall a simple question.

If you were applying for a job today and submitted a certificate bearing one date, while another version of what purports to be the same certificate carried a different date and different signatures, what do you think your prospective employer would do?

They would ask you to explain yourself. They might even reject your application.

Yet today, serious questions remain about the exact certificate President Bola Tinubu presented to the Independent National Electoral Commission. One version reportedly says June 22, another June 27; questions have also been raised about the signatures and the description of the degree.

I am not asking you to accept my conclusion. I am asking something much simpler: if a young Nigerian would be required to explain such discrepancies before getting an ordinary job, why should the man seeking Nigeria’s highest job be exempt from the same standard?

That is part of the Nigeria we must change—a Nigeria where there is one standard for those in power and another for everyone else.

Now, I want everyone in this hall to do something else for me. Look to your left. Now look to your right. Remember the faces you have just seen, because the people sitting beside you are not strangers. They are your partners in one of the most important assignments before our generation: building a Nigeria that works for everyone.

I stand before you today not simply as a presidential candidate asking for your support. I stand before you as a Nigerian who believes that our yo

DA DUMI-DUMI: Atiku, Obi, Kwankwaso da Makinde za su gana a Abuja Daga WakiliyaManyan ‘yan adawa a siyasar Najeriya, Ati...
10/08/2026

DA DUMI-DUMI: Atiku, Obi, Kwankwaso da Makinde za su gana a Abuja

Daga Wakiliya

Manyan ‘yan adawa a siyasar Najeriya, Atiku Abubakar, Peter Obi, Rabiu Kwankwaso da Seyi Makinde na daga cikin waɗanda ake sa ran za su shiga tattaunawar da aka shirya yi a Abuja ranar 18 ga Agusta, 2026, domin duba yiwuwar haɗa kan jam’iyyun adawa gabanin zaɓen 2027.

Ƙungiyar G100 ce ta shirya taron, bayan ta ce ta gudanar da shawarwari na sirri da wasu shugabannin jam’iyyun adawa da ‘yan takarar shugaban ƙasa.

G100 ta ce manufar ita ce samar da babbar ƙawancen adawa, inda za a fifita muradun ƙasa a kan burin mutum.

Ta kuma yi gargadin cewa rarrabuwar kan ‘yan adawa na iya amfani ga masu mulki, yayin da haɗin kai zai ba ‘yan Najeriya wata dama ta samun gagarumar adawa a 2027.

Shin za a iya samun haɗin kan Atiku, Obi, Kwankwaso da sauran ‘yan adawa kafin 2027? 🤔

LIKE // SHARE & FOLLOW US => Wakiliya

Na isa Osogbo, babban birnin Jihar Osun, tare da tawagar abokan siyasata, domin nuna goyon baya ga ɗan takararmu na gwam...
10/08/2026

Na isa Osogbo, babban birnin Jihar Osun, tare da tawagar abokan siyasata, domin nuna goyon baya ga ɗan takararmu na gwamnan jihar, Dr. Najeem Folasayo Salaam (Iwaloye), da babbar jam’iyyarmu ta ADC, a babban taron rufe yaƙin neman zaɓenmu gabanin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar Asabar.

Mun zo ne domin ƙara haɗa kan magoya bayanmu da kuma yin kira na ƙarshe ga al’ummar Jihar Osun da su amince da ADC, su ba ta damar jagorantar jihar wajen samar da ingantaccen shugabanci, kyakkyawan mulki da kuma kyakkyawar makoma ga kowa -AA

In sha Allah ko sunso ko sunki kaine shugan kasa 2027 da yardar Allah
10/08/2026

In sha Allah ko sunso ko sunki kaine shugan kasa 2027 da yardar Allah

Daga komawarsa APC yau, Dr Mustapha Inuwa ya ce tun daga sama har kasa APC ce za ta lashe zaɓen ta a jihar Katsina
09/08/2026

Daga komawarsa APC yau, Dr Mustapha Inuwa ya ce tun daga sama har kasa APC ce za ta lashe zaɓen ta a jihar Katsina

TIRKASHI:  Rarara yadda kake cin mútuncin 'yan uwanka 'yan Arewa, kake zàgìn Malaman Addini tabbas haka ya nuna 'yan Are...
05/08/2026

TIRKASHI: Rarara yadda kake cin mútuncin 'yan uwanka 'yan Arewa, kake zàgìn Malaman Addini tabbas haka ya nuna 'yan Arewa tsoronka suke, amma ina fatan watarana tsau tsauyi yasa kayi waka ka Zàgèni, wallahi ako waye ya tsaya maka daga ranar zaka fahimci ba kowa ake taba mútuncinsa a zauna Lafiya ba.

Wani Gajeren Sakon Dino Malaye Kenan Bayan Ya Saurari Wakar Da Yayiwa Malam Kayi Rawa.

Dauda Kahutu Rarara Qramin Shakiyyi

Address

Barhim
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ADC Safana posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share