Bilhaqqi Media Links

Bilhaqqi Media Links Media Channel
(1)

Wata tsohuwar model daga ƙasar Masar mai suna Omaima Nelson ta samu hukuncin zaman gidan yari daga shekaru 28 har zuwa r...
22/05/2026

Wata tsohuwar model daga ƙasar Masar mai suna Omaima Nelson ta samu hukuncin zaman gidan yari daga shekaru 28 har zuwa rai bayan ta kashe mijinta tare da yanke gawarsa a ranar Thanksgiving a shekarar 1991 a birnin Costa Mesa.

Omaima, wacce ke da shekaru 23 a lokacin, ta kashe mijinta mai shekaru 56, mai suna William Nelson, bayan wata mummunar rigima da ta barke tsakaninsu a cikin gidansu, makonni kaɗan kacal bayan sun yi aure.

Bayan kisan, ta shafe kwanaki tana yanke gawar, tana ƙoƙarin ɓoye shaidu da kuma zubar da gawar.

An k**a ta ne bayan ta nemi wani mutum ya taimaka mata wajen kawar da shaidun laifin.

A lokacin shari’arta a shekarar 1993, Omaima ta ce ta aikata hakan ne domin kare kanta saboda azaba da cin zarafin jiki da kuma lalata da take fuskanta daga mijin nata. Amma masu gabatar da ƙara sun ce yadda aka yi wa gawar ya nuna cewa an shirya laifin tun da farko.

Daga ƙarshe kotu ta same ta da laifin kisan kai na mataki na biyu, kuma har yanzu tana tsare a gidan yarin mata na California.

An ƙi sakinta sau da dama, inda Hukumar Parole ta California ta ce har zuwa shekarar 2020 tana nan a matsayin barazana ga lafiyar jama’a.

Kashi 90 Cikin Ɗari Na Waɗanda S**a Samu Nasarar Lashe Zaɓukan Fidda Gwani A Takarkari Daban-daban A Jihar Katsina, Ba Z...
22/05/2026

Kashi 90 Cikin Ɗari Na Waɗanda S**a Samu Nasarar Lashe Zaɓukan Fidda Gwani A Takarkari Daban-daban A Jihar Katsina, Ba Zaɓi Na Ba Ne Ko Na Ce Dole Sai An Zaɓe Su, Mun Ji Ra'ayoyin Al'umma Ne, Saboda Masu Ruwa Da Tsaki Na Kowacce Karamar Hukuma, Su Aka Ba Dama Su Je Su Zauna, Su Yi Abinda Ya Dace, Zaɓe Mu Ke Son Mu Ci A Jam'iyyar APC Ba Wai Biyan Buƙatar Kanmu Ba, Cewar Gwamna Dikko Raɗɗa

Me Za Ku Ce

Tom-tom Na Aika A Siyo Min Saboda Muryata Ta Dashe A Wajen Taro, Sai Yaron Da Na Aika Ya Siyo Min Wata Alawar Daban, Bay...
22/05/2026

Tom-tom Na Aika A Siyo Min Saboda Muryata Ta Dashe A Wajen Taro, Sai Yaron Da Na Aika Ya Siyo Min Wata Alawar Daban, Bayan Na Sha Ta K**a Min Harshe, Sai Mutane Suke Kallon K**ar Na Sha Kwaya, Alhalin Ni Ban Taba Shan Kayan Maye Ba A Rayuwata, Ìnji Hon Alhassan Ado Doguwa

Ko Gaskiyane zancen Gwamna Mal Dikko Umar Radda Kashi 90 Cikin Ɗari Na Waɗanda S**a Samu Nasarar Lashe Zaɓukan Fidda Gwa...
22/05/2026

Ko Gaskiyane zancen Gwamna Mal Dikko Umar Radda Kashi 90 Cikin Ɗari Na Waɗanda S**a Samu Nasarar Lashe Zaɓukan Fidda Gwani A Takarkari Daban-daban A Jihar Katsina, Ba Zaɓi Na Ba Ne Ko Na Ce Dole Sai An Zaɓe Su, Mun Ji Ra'ayoyin Al'umma Ne, Saboda Masu Ruwa Da Tsaki Na Kowacce Karamar Hukuma, Su Aka Ba Dama Su Je Su Zauna, Su Yi Abinda Ya Dace, Zaɓe Mu Ke Son Mu Ci A Jam'iyyar APC Ba Wai Biyan Buƙatar Kanmu Ba, Cewa Gwamna Malam Dikko Raɗɗa

APC ta tabbatar da Jamilu Gwamna ɗantakarar gwamnan Gombe Saɓanin pro Isah Ali pantami
21/05/2026

APC ta tabbatar da Jamilu Gwamna ɗantakarar gwamnan Gombe Saɓanin pro Isah Ali pantami

Ban shan ƙwaya,Kuma Ba Na Neman Mata Da Wasu Masu Mulki Ke yi, alewa ce Nake Sha..Ni masoyin alewa neAlhassan Ado Doguwa
21/05/2026

Ban shan ƙwaya,Kuma Ba Na Neman Mata Da Wasu Masu Mulki Ke yi, alewa ce Nake Sha..

Ni masoyin alewa ne

Alhassan Ado Doguwa

ILIMI HASKEN RAYUWA: A Gida Ɗaya An Samu Farfesa Ɗaya Da Lauyoyi Huɗu Yadda Iyalan Alhaji Babakano Aliyu Jada, S**a Yi N...
21/05/2026

ILIMI HASKEN RAYUWA: A Gida Ɗaya An Samu Farfesa Ɗaya Da Lauyoyi Huɗu

Yadda Iyalan Alhaji Babakano Aliyu Jada, S**a Yi Nasara Sak**akon Jajircewarsu Da Hazaƙarsu, Inda Allah Ya Albarkaci Zuri'arsa Da Samu Farfesa Ɗaya Da Kuma Lauyoyi Guda Huɗu, A Cikin Su Akwai

Farfesa Mohammed Babakano Aliyu Jada

Barista Fadimatu Babakano Aliyu Jada

Barista Adamu Babakano Aliyu Jada

Barista Hadiza Babakano Aliyu Jada

Barista Bilkisu Babakano Aliyu Jada

Wace Irin Fata Za Ku Yi Masa?

Arsenal ta lashe kofin ne bayan Man City ta yi canjaras 1-1 a wasanta da Bornemouth a yau Talata. Wannan ne karon farko ...
19/05/2026

Arsenal ta lashe kofin ne bayan Man City ta yi canjaras 1-1 a wasanta da Bornemouth a yau Talata.

Wannan ne karon farko da Arsenal ta lashe kofin tun 2004 ƙarƙashin jagorancin Arsene Wenger.

Yaya kuke ji da wannan labari?

Minista Muttaqha Rabe Darma ya bada sama da N1,072,000 domin biya wa dalibai 33 kudin zana jarabawar NECO  a Katsina.Min...
18/05/2026

Minista Muttaqha Rabe Darma ya bada sama da N1,072,000 domin biya wa dalibai 33 kudin zana jarabawar NECO a Katsina.

Minista Gidaje da raya birane na Najeriya, injiniya Muttaqha Rabe Darma, ya biya wa daliban 33 da basu samu nasarar cin jarabawar samu damar rubuta NECO ba, kudin zauna jarabawar har kimanin N1,072,000.

Mataimaki na musamman, ga Ministan Alhaji Gambo Garba ne ya jagoranci tawagar da ta wakilci Ministan zuwa makarantar yan Mata ta WTC da ke cikin birnin Katsina domin mika kudin ga shugabar makarantar, Hajiya Hadiza Nasir.

Gambo Garba, ya ce, bisa la'akari da rokon da shugabar makarantar ta rubuta cewa, tana rokon Injiniya Darma da ya shigo cikin lamarin yaran tare kuma da duba irin halin da wasunsu suke ciki na maraici da yanayin rayuwa, ya sa Ministan bai bata lokaci ba wajen aiko da sakon don abiya masu kudin su ci gaba da karatunsu.

Ya ce hakika Injiniya Darma, mutum ne mai matukar son ya ga matasa sun samu ilimi domin da shi ne ake samun ci gaba tare da zama nagartattun mutane da zasu amfani al'umma.

A nata jawabin jim kadan bayan karbar tallafin kudin, shugabar makarantar, Hajiya Hadiza Nasir, ta bayyana jin dadinta da godiya ga Injiniya Muttaqha Rabe Darma, musamman yadda ta ce daliban na son su ci gaba da karatunsu, kuma suna da kokari saidai babu yadda zasu yi.

Hadiza Nasir, ta ce, ba shi kadai ta bukaci ya shigo cikin lamarin yaran ba, ta ce ta nemi mutane da dama su shigo su taimaki daliban ko don kar rayuwarsu ta susuce.

Saidai ta ce, Muttaqha Rabe ne kadai mutumen da ya saurari koken na ta ya kuma biya wa daliban kudin don ci gaba da karatu.

Ta ce hakika, tana jin labarin irin ayyukan alherin da yake ga al'umma, kuma yau ita ma ga ta ta sheda tunda an zo har ofishinta an biya wa dalibanta kudin zauna jarabawa.

In za a iya tunawa dai Gwamnatin jihar Katsina na biya wa daliban kudin zana jarabawar amma sai wadanda s**a samu nasarar cin jarabawar samu damar rubuta NECO din.

An Yi Tattakin Mutane Milyan Biyar A Kano Domin Nuna Goyon Bayansu Ga Kwankwaso
18/05/2026

An Yi Tattakin Mutane Milyan Biyar A Kano Domin Nuna Goyon Bayansu Ga Kwankwaso

Da Dumi Dumi Kotu ta bayar da belin El-Rufai kan Naira miliyan 100Wata babbar kotu da ke Abuja ta bayar da beli ga tsoho...
18/05/2026

Da Dumi Dumi

Kotu ta bayar da belin El-Rufai kan Naira miliyan 100

Wata babbar kotu da ke Abuja ta bayar da beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zargin karan tsaye ga tsaron kasa da ake yi masa.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta bayyana cewa an bayar da belin ne kan kudi Naira miliyan 100, tare da sharadin cewa wanda zai tsaya masa dole ne ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro da ke Abuja.

Address

Katsina
820252

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bilhaqqi Media Links posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Bilhaqqi Media Links:

Share