RMC Hausa

RMC Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from RMC Hausa, Media Agency, Kofar Kaura Opposite Kiddies School Layout Katsina, Katsina.

Cin Zarafin Dan Jarida: SSR na Gwamnan Kano ya nemi afuwar yan jaridaGwamnatin Jihar Kano tare da SSR na Gwamna Abdullah...
26/02/2026

Cin Zarafin Dan Jarida: SSR na Gwamnan Kano ya nemi afuwar yan jarida

Gwamnatin Jihar Kano tare da SSR na Gwamna Abdullahi Rogo sun bai wa ’yan jarida hakuri kan zargin cin mutuncin daya daga cikin mambobinsu, bayan wani zaman sulhu da aka gudanar domin warware rikicin.

Sulhun ya biyo bayan zaman da Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya kira a ranar Laraba domin daidaita al’amuran da s**a lalace tsakanin bangarorin.

Taron ya samu halartar shugabannin kungiyar Kano Online Media Chapel karkashin jagorancin shugabanta, Comrade Abubakar Abdulƙadir Dangambo, da daraktocin Ma’aikatar Yada Labarai, tare da dan jarida kuma tsohon shugaban ƙungiyar ƴan jaridu ta ƙasa, Comrade Abdullahi Datti Arzai.

Da yake jawabi yayin taron, Kwamishina Waiya ya bukaci SSR Rogo da sauran jami’an gwamnati da su rika kyautata alaka da ’yan jarida domin ci gaban jihar. Ya kuma jaddada kudirin gwamnati na ci gaba da aiki kafada da kafada da kafafen yada labarai, yana mai amincewa da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen wayar da kan al’umma kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

A nasa bangaren, Shugaban Kano Online Media Chapel, Comrade Abdulƙadir Dangambo, ya gode wa kwamishinan bisa saurin shiga tsakani da ya yi wajen warware matsalar. Sai dai ya nuna cewa ba wannan ne karo na farko da ake zargin SSR Rogo da irin wannan hali ba, lamarin da ya bayyana a matsayin abin takaici.

Ya kuma ja hankalin jami’an gwamnati da su fahimci muhimmiyar rawar da ’yan jarida ke takawa a cikin al’umma da kuma tasirin aikinsu wajen inganta dimokuradiyya da gaskiya.

Lamarin dai ya zo ne a daidai lokacin da kungiyoyin kare hakkin dan Adam na cikin da wajen kasar nan s**a yi Allah wadai da faruwar al’amarin, tare da bai wa gwamnatin jihar wa’adin sa’o’i 24 ta dauki mataki ko kuma su dauki matakin shari’a.

Bangarorin sun bayyana fatan cewa sulhun da aka cimma zai taimaka wajen gyara alaka da kuma kauce wa maimaita irin wannan lamari a nan gaba.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN:Allah yayiwa  Shugaban Hukumar Samar Da Ruwan Sha Ta Jihar Katsina (Katsina State Wat...
26/02/2026

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN:

Allah yayiwa Shugaban Hukumar Samar Da Ruwan Sha Ta Jihar Katsina (Katsina State Water Board) Dakta Tukur Hassan Tingilin Ya Rasuwa.

Ya rasu Sakamakon Haďarin Mota Da Ya Rutsa Da Shi Da Yammacin Yau Alhamis

Allah Ya Jikansa Da Rahama!

A Cikin Mawaƙa Sarkin Waƙane Kaɗai Zaka Mishi Liki Da Ƴan N200 Shi Kuma Ya Zaro Ƴan N1000 Ya Liƙa Maka
31/12/2025

A Cikin Mawaƙa Sarkin Waƙane Kaɗai Zaka Mishi Liki Da Ƴan N200 Shi Kuma Ya Zaro Ƴan N1000 Ya Liƙa Maka

An Kafa Tubalin Sabuwar Kungiyar KATSINA YOUTH MOVEMENT TINUBU/DIKKO 2027 Domin Kawo Hadin kawunan Yan Jihar Katsina Dom...
31/12/2025

An Kafa Tubalin Sabuwar Kungiyar KATSINA YOUTH MOVEMENT TINUBU/DIKKO 2027 Domin Kawo Hadin kawunan Yan Jihar Katsina Domin Bada karin Damar Malam Dikko Radda Da Shugaban Kasa Tinubu Cigaba Da Ayyukan Alherin Da Sukeyi.

Kungiyar KATSINA YOUTH MOVEMENT TINUBU/DIKKO Na Cigaba aikin ta Karkashin Jagorancin Mai Baiwa Gwamnan Jihar Katsina Shawara Akan Yada Labaru A Shiyyar Katsina Ta Tsakiya Hon. S.A Abubakar Sani Dan-Abba.

Kamar yadda muka ruwaito S.A. Abubukar Dan-Abba ya kafa wannan kugiyar ne domin kara hadin kan al'umma musanman matasa na fadin Jihar ta Katsina baki daya.

Haka zalika domin wayarwa jama'a kawuna akan muhimman abubuwan cigaba da gwamnatocin jihar katsina karkashin jagorancin Gwamna Dikko Umar Radda phD da gwamnatin tarayya ke gudanarwa a Fadin Najeriya baki daya a karkashin shugaban cin Alhaji Ahmed Bola Tinubu.

Kungiyar na maraba da dukkanin masu kishin jihar Katsin da Kasa bakiya daya, domin samun goyon al'umma don cigaban Shugaban cin Tinubu Ahned Da Gwamna Dikko Radda Na Katsina a 2027.

SPONSORED:
S.A Abubakar Sani Dan-Abba.

Gwamnan jihar Neja Muhammad Umar Bago da mataimakinsa Comrade Yakubu Garba yayin da ake basu horon wucin gadi na yanda z...
25/12/2025

Gwamnan jihar Neja Muhammad Umar Bago da mataimakinsa Comrade Yakubu Garba yayin da ake basu horon wucin gadi na yanda za su sarrafa bindiga da kuma saitin harɓi a ziyarar da su ka kai sansanin da ake ba horar da jami'an tsaron gandun dajin jihar.

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa Ya Ƙaddamar Da Raba Kayan Aikin Gona Na Zamani Da Na Kwashe Shara Da Kuma ...
25/12/2025

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa Ya Ƙaddamar Da Raba Kayan Aikin Gona Na Zamani Da Na Kwashe Shara Da Kuma Manyan Motocin Na Shirin Nan Na Bankin Duniya (ACReSAL) Yau Laraba A Ma'aikatar Muhalli Dake Cikin Garin Katsina

HOTUNA: Yadda Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, Tare Da Dr. Rabi'u Musa Kwankwaso, Da Mukarabban Gwamnatin Jih...
25/12/2025

HOTUNA: Yadda Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, Tare Da Dr. Rabi'u Musa Kwankwaso, Da Mukarabban Gwamnatin Jihar Kano Baki Daya. Sun Halarci Jana'izar Dan Majalisar Jihar Kano, Aminu Sa'ad Ungogo Wanda Yake Wakiltar Karamar Hukumar Ungogo Ta Jihar Kano

Rana24

Kansila mace ɗaya tilo da aka zaɓa makonni biyu da su ka gabata a Legas ta rasuOluwakemi Rufai, Kansila mai wakiltar maz...
14/08/2025

Kansila mace ɗaya tilo da aka zaɓa makonni biyu da su ka gabata a Legas ta rasu

Oluwakemi Rufai, Kansila mai wakiltar mazaɓar C1 a ƙaramar hukumar Ibeju-Lekki, a jihar Legas, ta rasu bayan makonni biyu kacal da zabenta.

Rufai, ita ce mace ɗaya tilo da aka rantsar a kwanan nan a majalisar dokoki ta Ibeju-Lekki, kuma ta rasu ne da safiyar jiya Laraba bayan gajeriyar rashin lafiya.

A wata sanarwa da aka fitar, Seye Oladejo, mai magana da yawun jam’iyyar APC ta jihar Legas, ya bayyana Rufai a matsayin “ƙwararriya mai tasowa wadda ta nuna jajircewa, hidima ga jama’a a matakin ƙasa, da kuma goyon bayan shigar mata cikin siyasa.”

Oladejo ya miƙa ta'aziyyar jam'iyyar ga iyali da ma al'ummar mazaɓar ta baki ɗaya.

TALLA:Hukumar Gudanarwar Makarantar Alfijir Science International School Kankara  na sanar da Al'umma ta fara raba tikit...
14/08/2025

TALLA:
Hukumar Gudanarwar Makarantar Alfijir Science International School Kankara na sanar da Al'umma ta fara raba tikitin shiga Makarantar amatakan Renon Yara da kuma dana firamare na shashen karatun 2025/2026.

Ga masu bukata zasu iya tuntubar Wadannan Lambobin waya 09019199370-07035555275 - 07032340606.

Tinubu zai yi tafiya zuwa ƙasashen Japan da Brazil Shugaba Bola Tinubu zai kai ziyara zuwa ƙasashe biyu, Japan da Brazil...
14/08/2025

Tinubu zai yi tafiya zuwa ƙasashen Japan da Brazil

Shugaba Bola Tinubu zai kai ziyara zuwa ƙasashe biyu, Japan da Brazil a yau Alhamis, 14 ga watan Agusta.

Bayo Onanuga, mashawarcin shugaban ƙasa na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, ya ce Tinubu zai tsaya a Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), kafin ya zarce zuwa Japan.

Ana sa ran shugaban zai halarci taron ƙasa da ƙasa na tara kan ci gaban Afirka (TICAD9) a birnin Yokohama na ƙasar Japan daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Agusta.

Onanuga ya ce Tinubu zai kuma gudanar da tarukan tattaunawa tsakanin ƙasashe da kuma ganawa da shugabannin manyan kamfanonin Japan da ke da hannun jari a Najeriya.

“Bayan kammala taron TICAD9, Shugaba Tinubu zai tafi birnin Brasilia, babban birnin Ƙasar Tarayyar Brazil, domin ziyarar ƙasa ta tsawon kwanaki biyu daga Lahadi, 24 ga watan Agusta, zuwa Litinin, 25 ga watan Agusta,” in ji sanarwar.

“Wannan ya biyo bayan gayyatar da shugaban ƙasar Brazil, Luiz Inácio Lula da Silva, ya yi masa.”

Jarumin finafinai Hausa Ali Nuhu ya gana da gwamnan jihar Gombe Alhaji Inuwa Muhammad Yahaya a gidan gwamnatin Gombe Dag...
14/08/2025

Jarumin finafinai Hausa Ali Nuhu ya gana da gwamnan jihar Gombe Alhaji Inuwa Muhammad Yahaya a gidan gwamnatin Gombe

Daga cikin batutuwan da s**a tattauna harda yadda za a samarwa da matasa aikin yi

Address

Kofar Kaura Opposite Kiddies School Layout Katsina
Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when RMC Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category