12/04/2026
Tsaro!!!
Shugaban Karamar Hukumar Katsina, Hon. Isah Miqdad AD Saude, ya samar da fitilu masu amfani da hasken rana sama da guda ashirin ga al’ummar unguwannin Shararar Pipes da Farin Masallaci, dake cikin Mazabar Wakilin Kudu III, a wani mataki na inganta tsaro da walwalar al’umma, musamman a lokutan dare.
An gudanar da bikin kaddamar da fitilun ne karkashin jagorancin Kansilan Mazabar, Hon. Abdullahi Yusuf, tare da hadin gwiwar Kansila mai kula da sashen lafiya, Hon. Kabir Jimaita, wanda shima dan asalin yankin ne.
A yayin taron, Hon. Abdullahi Yusuf ya bayyana cewa wannan tallafi na daga cikin kokarin da Shugaban Karamar Hukumar ke yi wajen dakile matsalolin tsaro, musamman duba da yadda yankin ya fuskanci kalubale irin su fashin wayoyi, rikice-rikicen dare, da sauran ayyukan bata-gari.
Ya kara da cewa za a girke fitilun a wurare daban-daban masu muhimmanci domin tabbatar da ingantaccen tsaro da walwala ga al’ummar yankin.
A nasa jawabin, Hon. Kabir Jimaita ya yabawa Shugaban Karamar Hukumar bisa saurin daukar mataki wajen sauraron koken al’umma da kuma samar da wannan muhimmin tallafi cikin kankanin lokaci.
Taron ya samu halartar Kansila mai kula da sashen ayyuka na Karamar Hukumar Katsina, Hon. Engr. Abubakar Jafaru, tare da sauran manyan baki da al’umma da dama.
Zaharaddeen Muazu Rafindadi
Sakataren yada Labarai na Shugaban Karamar Hukumar Katsina.
11.04.26