Usman Abu Salman

Usman Abu Salman [LIFE IS TEMPORARY]
Divisional organising secretary at first aid group of jibwis (lagos mainland).

(CEO)USMAN ABU SALMAN VENTURES & ZAIMAN MULTI-TRADE GLOBAL ENTERPRISES

First aider
Health personnel
Graphic designer
Trading
Digital creator

16/09/2025

Allah ya gafarta maka baba.

INNA'LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Allah Ya Yi Wa Daraktan  Agaji Na Jahar Katsina Rasuwa,Alhaji Abdullahi I.N BakoriAl...
16/09/2025

INNA'LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN
Allah Ya Yi Wa Daraktan Agaji Na Jahar Katsina Rasuwa,

Alhaji Abdullahi I.N Bakori

Allah ya gafarta masa kuskuren sa.

08/09/2025

Fassarar iyyaka na'abdu wa iyyaka nasta'in

Shugaban kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa’ikamatis Sunnah Imam Dokta Abdullahi Bala Lau , Shugaban majalisar malamai...
02/09/2025

Shugaban kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa’ikamatis Sunnah Imam Dokta Abdullahi Bala Lau , Shugaban majalisar malamai Dokta Ibrahim Jalo Jalingo da daraktan ‘yan agaji Injiniya Mustapha Imam Sitti na farin cikin gaiyatar jama’a zuwa wa'azin ƙasa a garin kaduna tare da gagarumin taron gabatar da fassarar littafin WHERE I STAND “nan ne matsaya ta” da Sheikh Abubakar Mahmud Gumi ya wallafa da Dokta Ibrahim Jalo Jalingo ya fassara zuwa Larabci. Sai littafin AL’AKIDATUS SAHIHA, AHALARI, IZZIYYA, RISALA da ISHMAWI da Dokta Jalo ya juya daga zube zuwa wake.

Za a gudanar da gabatarwar ranar asabar 6 ga watan nan na Satumba 2025 da karfe 9am a dakin taro na Umaru Musa ‘YAR’ADUA HALL da ke Murtala Muhammed Square Kaduna.

Babban bako na musamman, mai girma shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu GCFR

Mai masaukin baki, Gwamnan jihar Kaduna Sanata Uba Sani

Iyayen taro mai alfarma Sarkin musulmi Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar da mai martaba Sarkin Zazzau Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli

Babban mai gabatarwa Sanata Dokta Abdul’aziz Yari

Mai bitar littattafan babban limamin masallacin Sultan Bello Sheikh Muhammad Sulaiman.

Sai Dokta Ahmad Gumi zai yi magana a madadin iyalan marigayi Sheikh Abubakar Mahmud Gumi.

Manyan baki gwamnoni, shugabannin kamfanoni, tsoffin gwamnonin jihar Kaduna Dokta Ahmed Muhammad Makarfi, Dokta Ramalan Yero da Malam Nasiru Elrufai sai kuma almajirai da daliban marigayi Sheikh Abubakar Mahmud Gumi.

Kazalika, kungiyar na gaiyatar jama’a zuwa taron karawa juna ilimi da tambayoyi da amsoshi kan illar masu ikirarin bin Kur’ani zallah wato ‘yan Ƙala ƙato da za a gabatar a dakin taro na Umaru Musa ‘Yar adua da ke Murtala Square Kaduna ranar Jumma’a 5 ga watan nan na Satumba 2025 daga bayan sallar la’asar.

Dokta Ibrahim Disina zai jagoranci taron da kulawar shugaban bita da taruka na kasa Dokta Abubakar Abdulsalam Baban Gwale. Masu jawabi sun hada da Sheikh Lawal Shu’aib Triump, Sheikh Abubakar Mazan Kwarai da Sheikh Musa Muhammad Dankwano.

Gabanin nan kwa

Hotuna: Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau.Majlisar Malamai...
24/08/2025

Hotuna: Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Bala Lau.

Majlisar Malamai ta kasa, (Nigerian council of Ulama) Ta ziyarci Shugaban IZALA Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau a ofishinsa dake sakateriyar kungiyar dake babban birnin tarayya Abuja.

Malaman da s**a fito daga kungiyoyin addinin musulunci, sunce manufar ziyarar shine Hadinkai tsakanin musilmi, domin a samu fahimtar juna da hada karfi da karfe domin tunkarar maunfofin musulunci a dukkan lamura.

Jibwis Nigeria

Sarkin Musulmi ya aiyana ranar Litinin 25 ga watan Agusta ta zama 1 ga watan Rabi'ul Auwal 1447.Shugaban kwamitin bayar ...
24/08/2025

Sarkin Musulmi ya aiyana ranar Litinin 25 ga watan Agusta ta zama 1 ga watan Rabi'ul Auwal 1447.

Shugaban kwamitin bayar da shawara kan harkokin addinin musulunci a Majalisar Sarkin Musulmin kuma Wazirin Sakkwato Farfesa Sambo Wali Junaid ya fitar da bayanin cewa ba a samu ganin jinjirin watan Safar ba a ranar Asabar a Najeriya.

"Kwamitin Ganin Wata na Ƙasa da na Harkokin Addini a Majalisar Sarkin Musulmi ba su samu bayanin fitar sabon watan Rabi'ul Auwal ba a ranar Asabar 29 ga watan Safar.

“Dob haka Lahadi 24 ga watan Agusta za ta zama 30 ga watan Safar 1447," a cewarsa.

Ya ƙara da cewa Sarkin Musulmi ya aiyana Litinin a matsayin farkon watan Rabi'ul Auwal bayan amincewa da rahoton rashin ganin wata da aka bayar.

Aminiya

First Aid Group of Jibwis Nigeria New books on Humanitarian Work published by the First Aid Group of Jibwis Nigeria were...
24/08/2025

First Aid Group of Jibwis Nigeria New books on Humanitarian Work published by the First Aid Group of Jibwis Nigeria were launched at the national council's grand meeting held yesterday, Saturday, in the city of Lokoja, Kogi State.

The books have been updated to gain more recognition and to translate the First Aid book into English for other parts of Nigeria and foreign countries.

"The first book is" First Aid to patient "Book Two" (2) Rules and hierarchy system (Classification of Ranks)

Tini, the Executive Director of the International Relief Council (Jibwis Nigeria) Engr. Sheikh Mustapha Imam Sitti He ordered that they be distributed to all states in Nigeria and abroad so that they can reach the Aid Workers to learn about the work.

Best wishes to this blessed Relief Assembly from top to bottom.

First Aid Group of Jibwis Nigeria August 24, 2025

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!! Ana sanar da Al'umma musulmai musamman mazauna chikin garin Yola chewa Shugaban JIBWIS NIG...
19/08/2025

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

Ana sanar da Al'umma musulmai musamman mazauna chikin garin Yola chewa Shugaban JIBWIS NIGERIA Shaikh Abdullahi Bala Lau zai gabatar da nasiha ta musamman Yau Talata 19 ga watan August tsakanin Magrib zuwa Isha a Masallachin Marigayi Modibbo Lamido dake nan chikin Yola.

Kazalika zamu kawo muku kaitsaye ta Dukkan shafukan Jibwis Nigeria .

Allah ya bada Ikon halarta dakuma sauraro.

JIBWIS NIGERIA

Kungiyar ɗalibai Musulmi ta MSSN dake Jami'ar tarayya kashere ta karrama Shugaban Izala.Kungiyar ɗalibai Musulmi ta MSSN...
18/08/2025

Kungiyar ɗalibai Musulmi ta MSSN dake Jami'ar tarayya kashere ta karrama Shugaban Izala.

Kungiyar ɗalibai Musulmi ta MSSN dake jami'ar tarayya ta kashere a jahar Gombe,(Federal University of Kashere) ta karrama Shugaban Izala na tarayyar Najeriya, Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau a ƙoƙarin da suke na yaɗa da'awa a cikin ƙasa da wajen ta. Karramawar bata tsaya kan shugaban shi kaɗai ba, harda babban sakataren ƙungiyar Sheikh Dr. Muhammad Kabir Haruna Gombe, kazalika MSSN ta karrama wasu daga cikin su masu ƙoƙari a cikin ya'yan Kungiyar, inda ta gayyato shugaban majalisar Malamai Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo, da daraktan agaji Engr Mustapha Imam Sitti, da shugaban Izala Na jahar Gombe Sheikh Salisu Muhammad Gombe s**a karrama su.

Taron ya samu halartan shugaban Jami'ar da rijistara da sauran jiga-jigan malamai daga jami'ar.

Jibwis Nigeria

AY ABUN DAGA ALLAH NEKO MAKIYANKU IDAN SUN GANKU SAI KUNBASU SHA'AWA.
11/08/2025

AY ABUN DAGA ALLAH NE

KO MAKIYANKU IDAN SUN GANKU SAI KUNBASU SHA'AWA.

Address

No 4 Murtala Mohammed Way
Lagos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Usman Abu Salman posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share