Gobenmu media

Gobenmu media im abbakar dan masani from borno state Kwaya Kusar

05/06/2026
Na Kammala Jami'a A Yanzu Haka, Ina Matukar Bukatar Aure, Matashi Daga 25 Zuwa 35 In Ansamu Inaso.Inji Safiyya Aminu.
04/06/2026

Na Kammala Jami'a A Yanzu Haka, Ina Matukar Bukatar Aure, Matashi Daga 25 Zuwa 35 In Ansamu Inaso.

Inji Safiyya Aminu.

Gwamnatin Tarayya ta mayar da hedikwatar gudanarwa ta Hukumar National Agency for the Great Green Wall (NAGGW) daga Abuj...
04/06/2026

Gwamnatin Tarayya ta mayar da hedikwatar gudanarwa ta Hukumar National Agency for the Great Green Wall (NAGGW) daga Abuja zuwa Jihar Kano domin ƙarfafa ayyukan yaƙi da hamada da sauyin yanayi a Arewacin Najeriya.

Ministan Muhalli, Balarabe Abbas Lawal, ya bayyana cewa matakin na daga cikin dabarun gwamnatin tarayya na inganta aiki da kusantar hukumomin gwamnati zuwa yankunan da suke gudanar da ayyukansu.

Sabuwar hedikwatar hukumar za ta fara aiki daga harabar Afforestation Programme Coordinating Unit (APCU) da ke Kano, wanda gwamnati ta bayyana a matsayin wuri mai muhimmanci ga ayyukan hukumar a jihohin Arewa.

~ Rahama Kabeer Fagge
APC Senatorial Women Leader Kano State

FIYE DA MUTUM 4,000 SUN AMFANA DA TALLAFIN SHINKAFA DA KUDIN CEFA’NE NA SALLAH DA ALHAJI DAUDA KAHUTU RARARA YA RABA A G...
24/05/2026

FIYE DA MUTUM 4,000 SUN AMFANA DA TALLAFIN SHINKAFA DA KUDIN CEFA’NE NA SALLAH DA ALHAJI DAUDA KAHUTU RARARA YA RABA A GARIN KAHUTU

A wani gagarumin shirin tallafa wa al’umma gabanin shagalin Sallah, fiye da mutum dubu huɗu ne s**a ci gajiyar tallafin shinkafa da kuma kuɗin cefane naira dubu biyu-biyu da Sarkin Waka na Kasar Hausa, Alhaji Dauda Kahutu Rarara, ya raba a garin Kahutu da ke Karamar Hukumar Danja.

Tallafin ya haɗa da buhunan shinkafa tare da kuɗin cefane, wanda aka bayyana cewa an tsara shi ne domin rage wa jama’a raɗaɗin rayuwa tare da tabbatar da cewa suna gudanar da bukukuwan Sallah cikin walwala da jin daɗi.

Wannan tallafi dai ya zo a wani lokaci da jama’a ke fuskantar ƙalubalen rayuwa, inda aka ce zai taimaka matuƙa wajen rage wahalhalu musamman ga iyalai masu ƙaramin ƙarfi.

Al’ummar Karamar Hukumar Danja sun bayyana jin daɗi da godiya bisa wannan taimako, inda s**a ce irin wannan ɗaukar nauyi da nuna tausayi na ƙara ƙarfafa dankon zumunci tsakanin shugabanni da talakawa.

Bayan kammala rabon tallafin, Alhaji Dauda Kahutu Rarara ya yi kira ga masu hali da arziki da su riƙa taimaka wa mabukata, musamman a irin wannan lokaci na bukukuwa da jama’a ke buƙatar tallafi fiye da kowane lokaci.

Daga Mubarak Dabai

Tsohuwar ministar  jin ƙai da walwalar al’umma, Sadiya Umar Farouq, tana ƙasar Masar domin jinya kuma ba ta da ƙarfin ha...
19/05/2026

Tsohuwar ministar jin ƙai da walwalar al’umma, Sadiya Umar Farouq, tana ƙasar Masar domin jinya kuma ba ta da ƙarfin halartar kotu, in ji lauyanta.

‎Oladipo Okpesheyi, lauyan Sadiya Umar Farouq, ya ce wacce yake karewa tana ƙasar Masar a halin yanzu domin jinya, ba ta da karfin damar gurfana a gaban kotu ba.

Ana tuhumar Farouq tare da Bashir Nura Alkali, babban sakatare a ma’aikatar, da wani Sani Mohammed kan tuhume-tuhume guda 21 da s**a shafi cin amanar ƙasa da kuma amfani da mukami ba daidai ba, kamar yadda Hukumar EFCC ta shigar.

Tsohuwar jarumar Kannywood kuma matar fitaccen jarumi Adam A Zango Maimuna tare da mahaifiyarsa a hanyarsu ta zuwa ƙasar...
18/05/2026

Tsohuwar jarumar Kannywood kuma matar fitaccen jarumi Adam A Zango Maimuna tare da mahaifiyarsa a hanyarsu ta zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da ibadar aikin hajjin bana.

Wane irin fata za ku yi musu?

Yadda Jami'an NDLEA S**a Shiga Cikin Kogo Domin Farautar Masu Harkàr Miyagùn Ƙwayoyi A Yankin Rimin Keɓe Dake Kano, Inda...
15/05/2026

Yadda Jami'an NDLEA S**a Shiga Cikin Kogo Domin Farautar Masu Harkàr Miyagùn Ƙwayoyi A Yankin Rimin Keɓe Dake Kano, Inda Aka K**a Mutane 19 Tare Da Ƙwato Kayan Maye Kala-Kala

A Ƙarshe An̈ Gano Cewa Sace Amirah Aka Yi A KanoKwana uku da s**a wuce ne aka fara cigiyar Amirah, bayan am aike ta daga...
14/05/2026

A Ƙarshe An̈ Gano Cewa Sace Amirah Aka Yi A Kano

Kwana uku da s**a wuce ne aka fara cigiyar Amirah, bayan am aike ta daga Sauna zuwa Hatoro amma ba ta koma gida ba tun ranar.

Wanda hakan ya sa aka bada cigiyarta, saidai daga baya ƴan uwanta sun sanar da cewar dauke ta aka yi, kuma har an fara magana da waɗanda s**a ɗauke ɗin.

An sace ta ne a tsakanin Sauna zuwa Hotoro dake ƙaramar hukumar Nasarawa a Kano bayan an aike ta.

Allah Ya kuɓutar da itam

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban ƙasar Koriya ta Arewa Kim Jong ya baiwa 1ran wasu manyan  makamai masu linzami na nahiyoyi (ICBMs...
09/05/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban ƙasar Koriya ta Arewa Kim Jong ya baiwa 1ran wasu manyan makamai masu linzami na nahiyoyi (ICBMs) har guda 500, nau’in Hwasong-18, rahotanni sun ce bayan makamaπ sun fito daga ƙasar Koriya ta Arewa daga nan sun je hannun China da Rasha sannan aka taho da su 1rán ta hanyar tekun Caspian.

Rahotannin sun ƙara da cewa waɗannan makamai na da matuƙar nisa, inda za su iya kai hari zuwa manyan biranen ƙasar Am0rka irinsu New York ko Washington DC.

Ku bayyana mana ra'ayinku.

kamun inma lest go
09/05/2026

kamun inma lest go

Address

Kwaya Kusar
Maiduguri

Telephone

+2348103800353

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gobenmu media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gobenmu media:

Share