Jaridar Tijjaniyya

Jaridar Tijjaniyya Jaridar Tijjaniyya, Kamfani Ne Me Zaman Kanshi Dake Yada Akidar Tijjaniyya Da Kuma Faidha.

ALHAMDULLILAH TAFSIR 01 COMPLETEBY OUR LEADER OUR FATHER SHEIKH IMAM MODIBBO HASHIMU GIREI RAMADAN KAREEM ✍️
20/02/2026

ALHAMDULLILAH TAFSIR 01 COMPLETE
BY OUR LEADER OUR FATHER SHEIKH IMAM MODIBBO HASHIMU GIREI RAMADAN KAREEM
✍️

Matashin Malamin Addinin Musulinci, Sayyid Abdussamad Usman Abdukadir Zari'a, Yayi Kira Ga Musulmin Duniya Da Su Kara Hi...
18/02/2026

Matashin Malamin Addinin Musulinci, Sayyid Abdussamad Usman Abdukadir Zari'a, Yayi Kira Ga Musulmin Duniya Da Su Kara Himma Da Jajircewa Akan Soyayyar Su Da Manzan Allah SAW.

Sayyid Abdussamad, Yayi Wannan Kiran Ne A Yau Laraba 1 Ramadan, A Lokacin Da Yake Gabatar Da Tafsirin Al'qur'ani Mai Girma A Garin Zariya.

Abdussamad, Ya Kara Jan Hankalin 'Yan Uwa Musulmi Da Su Kasance Masu Nuna Kishin Su Da Kaunar Su Ga Manzan Allah Fiye Da Komai Na Rayuwar Su Ta Duniya Da Lahira.

Daga Karshe Ya Jaddada Ma Al'umma Cewa, Kaunar Annabi Muhammad SAW, Tare Da Bin Umarnin Sa Sune Kadai Abinda Mutum Ze Rike Ya Tsira Gaban Allah A Ranar Gobe Kiyama.

CIKAKKEN RAHOTO AKAN SHARI’AR MAULANA KHALEEFA BAYAN FITOWA KAFIN KOMAWA KARFE 2:00pm...Bincike Tare Da Bin Kwakkwafi Su...
12/02/2026

CIKAKKEN RAHOTO AKAN SHARI’AR MAULANA KHALEEFA BAYAN FITOWA KAFIN KOMAWA KARFE 2:00pm...

Bincike Tare Da Bin Kwakkwafi Sun Tabbatar Da Haleefa Beda Hannu Cikin Abinda Ake Zargin Shi Dashi, Sannan Babu Wata Hujja Ta Aka Gabatar A Gaban Kotu Wadda Take Da Tabbacin Zargin Da Ake Mashi...

Babban Kotun High Court Dake Babban Birnin Tarayya Abuja, A Zaman Da Aka Yi Ta Bawa Jami'in Soja Da Ya Bayar Da Umarnin A Tsare Khaleefa Awa Uku (3) Daga Karfe 11:am Zuwa 2pm, Domin Ya Gabatar Da Kwakkwarar Hujjar Dokar Da Tabashi Damar Cigaba Da Tsare Khaleefa Har Na Watanni Biyu...

Sakamakon Hakan Ne Ake Sa Ran Matuqar Jami'in Sojin Be Kawo Hujjar Cigaba Da Tsare Khaleefa Nan Da Awa (3) Ba, Kotun Zatayi Watsi Da Karar Sannan Ta Bayar Da Umarnin Sakin Khaleefa Nan Take...

ALLAH YABAMU NASARA...

Muftahu Yahaya Mai Dandarani ✍️
National Co-odinator Tafsir&Maulud Fityanu Media.

Da Lafiya sa Shekaru 107 Amma Sai Kagansa a Gida Yana Taƙawa, Ba Tare Da Ya riƙe Wani Sanda Ba Ko Waninsa RTA
01/02/2026

Da Lafiya sa Shekaru 107 Amma Sai Kagansa a Gida Yana Taƙawa, Ba Tare Da Ya riƙe Wani Sanda Ba Ko Waninsa RTA

Yanzu yanzu :-Manyan Khalifofin Zawiyoyin Gaidam Jihar YOBE sun yi Addua akan Allah ya kubutar da Sheikh Sani Khalifa Ab...
01/02/2026

Yanzu yanzu :-Manyan Khalifofin Zawiyoyin Gaidam Jihar YOBE sun yi Addua akan Allah ya kubutar da Sheikh Sani Khalifa Abdulqadeer Zaria daga Hannun Gwamnati cikin Aminci a filin Mauludi dake gudana yanzu haka.

Rahoto Daga Abuja: Tawagar Malaman Pakistan Sun Kai Ziyarar Alhini Ga Iyalan Sheikh Dahiru BauchiA daren Lahadi, 01/02/2...
01/02/2026

Rahoto Daga Abuja: Tawagar Malaman Pakistan Sun Kai Ziyarar Alhini Ga Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi

A daren Lahadi, 01/02/2026, Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi, Khalifatu Lisanul Faida, ya karɓi wata tawaga ta manyan baƙi daga ƙasar Pakistan a birnin Abuja. Baƙin sun iso ne domin miƙa girmamawa, ta’aziyya da jajen rasuwar Maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Ziyarar ta gudana cikin natsuwa da ɗaukaka, inda manyan malamai da dattawan Pakistan s**a bayyana alhini tare da yabawa da gagarumar gudummawar da marigayi Maulana ya bayar wajen bunƙasa addinin Musulunci a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

A jawabin maraba, Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi ya tarbi baƙin cikin ladabi da kwarjini, yana mai godiya bisa wannan ziyara ta alfarma. Ya jaddada muhimmancin ƙarfafa haɗin kan malamai da kuma ci gaba da adana gadon ilimi, tarbiyya da hidimar al’ummah da marigayi Maulana ya bari.

Ziyarar ta sake nuna girman darajar iyalan Maulana da majalisarsa a idon duniya, tare da tabbatar da cewa hasken tsattsarkan Faida ya wuce iyakoki, yana ci gaba da haskakawa a zukatan al’umma.

Khalifa Sayyid Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi, RTA Ya Tashi Daga Abuja Zuwa Yola Wajan Bude Masallacin Juma,a, Wanda Zai G...
29/01/2026

Khalifa Sayyid Ibrahim Sheikh Dahiru Bauchi, RTA Ya Tashi Daga Abuja Zuwa Yola Wajan Bude Masallacin Juma,a, Wanda Zai Gudana Gobe Juma,a 30/1/2026...

HUTUNAN WASU DAGA SHIKIN WANDA S**A HALARCI TARON MAULIDIYANDA MAULIDI YA GUDANA A NUMAN,MATASAN SHABBABU NABBIY SAW NUM...
15/01/2026

HUTUNAN WASU DAGA SHIKIN WANDA S**A HALARCI TARON MAULIDI
YANDA MAULIDI YA GUDANA A NUMAN,
MATASAN SHABBABU NABBIY SAW NUMAN LGA S**A GUDANARADA TARON MAULIDI. RANAN LITININ

MAKON SHEHU DAY 01A Yau aka Bude Makon Shehu R.T.A Na Mauludin Maulanmu Shehu Ibrahim Inyass Na Shekarar 2026 a Jihar Ka...
11/01/2026

MAKON SHEHU DAY 01

A Yau aka Bude Makon Shehu R.T.A Na Mauludin Maulanmu Shehu Ibrahim Inyass Na Shekarar 2026 a Jihar Katsina

Wannnan Taro Na Mauludin Shehu Ibrahim Inyass R.T.A Zai Gudanane Karkashin Kulawar Sheikh Dahiru Usman Bauchi Foundation da Majma'u Ahbabu Sheikh Ibrahim Inyass

Muna Rokon Allah Yadda aka Fara Wannan Taro Lafiya Allah Yasa a Gama lafiya.

Jaridar Tijjaniyya
11/01/2026

DA DUMI-DUMI: Yan Izala Na Yunkurin Rushe Masallacin 'Yan Darika Su Hada Da Nasu A Tudun Wada Zariya...'Yan Izala Suna Y...
07/01/2026

DA DUMI-DUMI: Yan Izala Na Yunkurin Rushe Masallacin 'Yan Darika Su Hada Da Nasu A Tudun Wada Zariya...

'Yan Izala Suna Yunkurin Rusa Masallacin Ne Saboda Suna Buqatar Fadada Nasu Masallacin, A Yayin Da S**a Siya Gidaje A Kusa Da Masallacin. Masallacin Da Suke Yunkurin Rusawa Beda Alaqa Da Wani Gida, Sakamakon Shekaru Fiye Da Sittin (60) Ana Ibada A Cikin Shi Tin Kafin Wasu Gine-Gine A Yankin...

'Yan Izalan Sun Ce Sun Siya Gida Ne Hade Da Masallacin Da Ya Ke Kusa Da Gidan, Bayan Kuma Addinin Musulinci Be Yarda Da Siyarwa Ko Gadar Masallaci Ko Kyautar Da Masallaci Ba...

Haka Zalika, 'Yan Izalan Sun Ce Zasu Ginawa 'Yan Darikan Wani Masallacin A Tsallake (Temporary) A Yayin Da 'Yan Darikan Basu Aminta Da Hakan Ba, Duba Da Wajen Ya Shiga Hanya, Kuma Suna Kallan Hakan A Matsayin Yaudara Da Kuma Kaskantar Da Masallacin. Tare Da Zaluntar Su....

Gamayyar Darikun Sufayen Sun Rubuta Koken Su Ga Duk Wata Hukuma Da Ta Ke Da Hakki A Yankin Domin Duba Al'amari Kamar Irin Su:--👇

1) Masarautar Zazzau
2) Office Din Hakimin Wajen Gari
3) D.P.O T/Wada Zariya
4) Sarkin T/Wada Zariya
5) Fityanul Islam
6) Majalisar Malamai Ta Tijjaniyya
7) Baba Trader Juma'at Mosque
8) Hisba
9) Mai Unguwa
10) Kungiyar Limaman Hamsussalawat T/Wada

Daga Karshe 'Yan Darikun Sun Sha Alwashin Rusa Masallacin Duk Wanda Ya Rusa Nasu Masallacin, Da Kuma Kare Kansu Daga Harin Duk Wanda Ze Rusa Musu Masallacin Su...

TOFAH : Wasu Matasa da dama a bangaren Izala Sun Nuna Damuwarsu Matuka akan Yadda akecin gyaran Babban Malamin su, Wato ...
07/01/2026

TOFAH : Wasu Matasa da dama a bangaren Izala Sun Nuna Damuwarsu Matuka akan Yadda akecin gyaran Babban Malamin su, Wato Malam Adam Abdallah, a karatuttuka daban-daban da s**a haɗa da Huɗubar Jumu'a, Karatun Tafsirin Alqur'ani, da Hadisi, dama sauran Littatafai gaba ɗaya.
Inda dayawa Malamin yake Wasu kura-kurai a ɓangaren Arabiyya, da kuma ɓata Fassarar Alqur'ani gabaki ɗaya. Wanda a wani Sa'in Malamin zai riƙa jan Baƙi, baƙi na Jansa a cikin karatuttuka daban-daban da yake gabatarwa a kafafen sada zumunta.

Dayawa daga cikin Mutane Mabiya Ɗarikar Tijjaniyya suna Ganin cewa Kura-kuran Malamin Sun fara bayyana ne a idon duniya, a sakamakon Cika baki da yayi na cewa Zai iya karantar da Shehu Tijjani, (Shugaban Ɗarikar Tijjaniyya na duniya gabaki ɗaya) harma Babban Khalifan sa (Shehu Ibrahim Inyass RTA)

A dalilin haka wasu daga cikin Mabiya Ɗarikar Tijjaniyya a garin Kano dama sauran Jihohi a Nigeria S**a fara bibiyar Malamin a kafafen sada zumunta a cikin karatuttukan sa suna cinsa gyara, tareda bayyanar da Jahilcin Malamin a idon Duniya gabaki ɗaya.

Daga cikin Matasan da suke cinsa gyara a Social media Mabiya Ɗarikar Tijjaniyya Sun haɗa da Shahararren hazikin matashin nan Sheikh Nibras da kuma Sheikh Shafi'u Yusuf.

A dalilin haka Mutane da dama a bangaren Izala da darika S**a shiga cikin damuwa tareda kira ga Malamin da ya koma Makarantar Zaure Domin ya Naƙalci karanta baƙi, tareda Sanin Arabiyya tukuna kafin Hawa mimbarin Malunta.

Shin masu sauraro me kuke gani Anya malam zai koma Makarantar Zaure ya gyara, ko kuma zai cigaba da hawa Mimbari a haka ?

Shin idan ya ɗauki wannan shawara Wane cigaba kuke ganin zai samu ?
Shin idan ya cigaba da hawa Mimbari a haka me zai faru ?

Rubutawa : Abubakar Shehu Dogondaji
07-01-2026 Wednesday

Babban Lauya A Nijeriya, Barr. Nazir Musa Aliyu Mai Yasin, Ya Caccaki Matakin Da Gwamnati Ta Dauka Akan Tsare Malamin Ad...
07/01/2026

Babban Lauya A Nijeriya, Barr. Nazir Musa Aliyu Mai Yasin, Ya Caccaki Matakin Da Gwamnati Ta Dauka Akan Tsare Malamin Addinin Musulinci Sheikh Sani Khalifa Zariya...

Barr. Nazir Musa Yace, A Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, Ba'a Yarda Da Tsare Mutum Fiye Awa 48 Ba, Indai Akwai Kotu Da Take Da Tazarar Kilo Mita 40 A Karkashin Dokar (1999 CONSTITUTION OF THE FEDERAL REPUBLIC OF NIGERIA)...

Barr. Nazir Musa, Ya Kafa Hujja Ta Daya Da Section 35(5), Hujja Ta Biyu Section 36(4)&(5), Hujja Ta Uku Day Case Din LOFADEJO V. JOHNSON @ Shekarar 2007 A Littafin 8 NWLR pt 1037 A Shafi Na 53, Hujja Ta Hudu Da Salux Populi Supreme Lex, Hujja Ta Biyar Da Wata Doka Fa Take Cewa Bazai Yiwu Kazama Mai Kara Ba Kuma Ka Zama Alkali...

Address

Sokoto

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Tijjaniyya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share