07/01/2026
TOFAH : Wasu Matasa da dama a bangaren Izala Sun Nuna Damuwarsu Matuka akan Yadda akecin gyaran Babban Malamin su, Wato Malam Adam Abdallah, a karatuttuka daban-daban da s**a haɗa da Huɗubar Jumu'a, Karatun Tafsirin Alqur'ani, da Hadisi, dama sauran Littatafai gaba ɗaya.
Inda dayawa Malamin yake Wasu kura-kurai a ɓangaren Arabiyya, da kuma ɓata Fassarar Alqur'ani gabaki ɗaya. Wanda a wani Sa'in Malamin zai riƙa jan Baƙi, baƙi na Jansa a cikin karatuttuka daban-daban da yake gabatarwa a kafafen sada zumunta.
Dayawa daga cikin Mutane Mabiya Ɗarikar Tijjaniyya suna Ganin cewa Kura-kuran Malamin Sun fara bayyana ne a idon duniya, a sakamakon Cika baki da yayi na cewa Zai iya karantar da Shehu Tijjani, (Shugaban Ɗarikar Tijjaniyya na duniya gabaki ɗaya) harma Babban Khalifan sa (Shehu Ibrahim Inyass RTA)
A dalilin haka wasu daga cikin Mabiya Ɗarikar Tijjaniyya a garin Kano dama sauran Jihohi a Nigeria S**a fara bibiyar Malamin a kafafen sada zumunta a cikin karatuttukan sa suna cinsa gyara, tareda bayyanar da Jahilcin Malamin a idon Duniya gabaki ɗaya.
Daga cikin Matasan da suke cinsa gyara a Social media Mabiya Ɗarikar Tijjaniyya Sun haɗa da Shahararren hazikin matashin nan Sheikh Nibras da kuma Sheikh Shafi'u Yusuf.
A dalilin haka Mutane da dama a bangaren Izala da darika S**a shiga cikin damuwa tareda kira ga Malamin da ya koma Makarantar Zaure Domin ya Naƙalci karanta baƙi, tareda Sanin Arabiyya tukuna kafin Hawa mimbarin Malunta.
Shin masu sauraro me kuke gani Anya malam zai koma Makarantar Zaure ya gyara, ko kuma zai cigaba da hawa Mimbari a haka ?
Shin idan ya ɗauki wannan shawara Wane cigaba kuke ganin zai samu ?
Shin idan ya cigaba da hawa Mimbari a haka me zai faru ?
Rubutawa : Abubakar Shehu Dogondaji
07-01-2026 Wednesday