11/06/2026
Ana ci gaba da samun saɓanin ra'ayi kan batun ficewar tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, daga jam'iyyar APC a Jihar Gombe.
Daily Trust ta rawaito cewa yayin da ɓangaren Pantami ke cewa ya ajiye takardar murabus dinsa daga APC kafin ya koma PDP tare da samun tikitin takarar gwamna na jam'iyyar, wasu shugabannin APC na mazabarsa ta Pantami sun musanta cewa ya bi wannan tsari kafin sauya sheƙa.
Shugaban APC na Mazabar Pantami da ke Karamar Hukumar Gombe, Alhaji Bala Galda, ya shaida wa manema labarai cewa shi da kansa ne ya karɓi takardar murabus ɗin Pantami.
A cewarsa, takardar mai ɗauke da kwanan watan 19 ga Mayu, 2026, ta samu karɓuwa daga gare shi tare da sanya tambarin yatsa, yayin da mai bai wa APC shawara kan harkokin shari'a a mazabar, Malam Babangida Gololo, ya sanya hannu a matsayin shaida.
Galda ya bayyana cewa bayan Pantami ya shiga PDP kuma ya samu tikitin takarar gwamna, shugabannin APC na ƙaramar hukuma sun umarci shugabannin mazabar da kada su karɓi ko su sanya hannu a kowace takardar murabus da zai gabatar.
Sai dai ya ce ya sanar da su cewa ya riga ya karɓi takardar tun kafin wannan umarni, yana mai cewa babu wata doka da ta wajabta masa sanar da shugabannin jam'iyya a matakin ƙaramar hukuma ko jiha idan wani memba ya yanke shawarar ficewa daga jam'iyyar.
Ya kuma zargi shugabannin jam'iyyar da neman ya musanta karɓar takardar, amma ya ƙi amincewa da hakan saboda a cewarsa gaskiya ce da ba zai iya musantawa ba.
Shi ma Malam Babangida Gololo ya ce babu wani tanadi a kundin tsarin mulkin jam'iyyar da ya wajabta wa talakan memba gabatar da rubutacciyar takardar murabus kafin shiga wata jam'iyya, yana mai cewa a aikace, shiga sabuwar jam'iyya na nuna mutum ya fice daga tsohuwar jam'iyyarsa.
Sai dai Sakataren Yaɗa Labarai na APC a Jihar Gombe, Moses Kyari, ya ce jam'iyyar ta bukaci shugaban mazabar ya gabatar da kwafin takardar murabus ɗin da aka karɓa, amma bai yi hakan ba.
Kyari ya kuma bayyana cewa bisa tsarin jam'iyyar, sakataren mazaba ne ya k**ata ya karɓi irin wannan takarda ba shugaban mazaba ba.
Ya ƙara da cewa har yanzu sun gayyaci shugaban mazabar domin ya gabatar da asalin takardar ko ya bayyana a gaban jam'iyyar, amma bai amsa gayyatar ba.
A cewarsa, har yanzu sunan Pantami yana cikin rajistar mambobin APC da ke kan tsarin INEC, yana mai jaddada cewa jam'iyyar ba ta hana shi ficewa ba, amma tana ganin ya k**ata a bi ƙa'idar da ta dace wajen yin hakan.