Africa Trust

Africa Trust Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Africa Trust, Kano.
(1)

Africa Trust Media Hub Ltd deliver first-class news and programmes grounded in objectivity, fairness, and accuracy, promoting equal opportunitie within its team and fostering inclusive engagement with diverse audiences [email protected]

Rahotanni daga sun bayyana cewa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid na ci gaba da tattaunawa mai zurfi domin ɗaukar ɗan...
11/06/2026

Rahotanni daga sun bayyana cewa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid na ci gaba da tattaunawa mai zurfi domin ɗaukar ɗan wasan tsakiya na ƙasar Portugal, Bernardo Silva.

Fabrizio Romano ya bayyana cewa Real Madrid ta shiga zawarcin ɗan wasan ne a ba`zata, yayin da take ƙoƙarin riga abokan hamayyarta Barcelona da kuma Atlético Madrid wajen kammala yarjejeniyar.

Rahotannin sun nuna cewa tuni shugabannin Real Madrid s**a aika da tayin farko zuwa ga wakilan Bernardo Silva, a wani mataki da ke nuna aniyar ƙungiyar na ganin ta samu sa hannun ɗan wasan kafin fara kakar wasa mai zuwa.

Haka kuma, an rawaito cewa José Mourinho, ya nuna goyon bayansa ga yiwuwar komawar Silva zuwa Santiago Bernabéu.

A cewar majiyoyin da ke kusa da tattaunawar, Real Madrid na da kwarin gwiwar cewa za ta iya kammala cinikin cikin nasara idan har tattaunawar ta ci gaba yadda ake fata.

Majalisar Dattawan Najeriya ta umarci hukumomin tsaro da su ƙara zage dantse wajen gano tare da cafke ’yan bindiga da ’y...
11/06/2026

Majalisar Dattawan Najeriya ta umarci hukumomin tsaro da su ƙara zage dantse wajen gano tare da cafke ’yan bindiga da ’yan ta’adda da ke amfani da kafafen sada zumunta, musamman TikTok, wajen nuna ayyukansu na laifi da kuma baje kolin kuɗaɗen da s**a samu ta haramtacciyar hanya.

Jaridar punch ta rawaito cewa matakin ya biyo bayan wani ƙuduri da Sanata Sunday Karimi ya gabatar a zauren majalisar kan ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga da matsalar tsaro a yankin Kogi ta Yamma da sauran sassan ƙasar.

Yayin zaman majalisar, Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi kira ga Cibiyar Yaƙi da Laifukan Yanar Gizo ta Rundunar ’Yan Sandan Najeriya da sauran hukumomin tsaro da su fara bibiyar tare da k**a mutanen da ke amfani da shafukan sada zumunta wajen tallata ayyukan ta’addanci.

Ta bayyana damuwarta kan yadda wasu ’yan bindiga ke bayyana kansu a fili a kafafen sada zumunta, suna nuna kuɗaɗen da s**a samu tare da gudanar da rabon kuɗi ga mabiyansu.

A cewarta, wasu ’yan bindiga sun gudanar da rabon kuɗi sama da naira miliyan 100 cikin ƙasa da mintuna 30 ta hanyar shafukan sada zumunta, lamarin da ya nuna cewa suna gudanar da ayyukansu ba tare da fargabar hukuma ba.

Da yake mayar da martani, Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana lamarin a matsayin babban ƙalubale ga hukumomin tsaro da kuma nuna rashin mutunta ikon gwamnati.

Ya ce ya k**ata jami’an Department of State Services da sauran hukumomin tsaro su yi amfani da bayanan da ke yawo a kafafen sada zumunta wajen gano waɗanda ke aikata laifukan da kuma gurfanar da su a gaban doka.

Akpabio ya kuma jaddada cewa nuna kuɗaɗe da ayyukan ta’addanci a kafafen sada zumunta wata hanya ce ta ƙalubalantar gwamnati da ƙoƙarin raunana amincewar jama’a ga tsarin tsaro.

Majalisar ta kuma buƙaci hukumomin tsaro da na leƙen asiri su ɗauki lamarin da muhimmanci tare da tabbatar da cewa an k**a masu aikata irin waɗannan laifuka domin tabbatar da doka da oda a ƙasar.

Rahotanni daga ƙasar Sufaniya sun bayyana cewa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta hana tsohon ɗan wasanta kuma tsohon...
11/06/2026

Rahotanni daga ƙasar Sufaniya sun bayyana cewa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta hana tsohon ɗan wasanta kuma tsohon kocinta, Xavi Hernández, damar bugawa ƙungiyar tsoffin taurarin kulob ɗin Barça Legends.

Fabrizio Romano ya rawaito cewa jaridar Diario AS ta ce Xavi ya nemi izinin shiga wasanni biyu na ƙarshe da Barça Legends za ta buga, amma shugabannin kulob ɗin sun ƙi amincewa da buƙatar tasa.

Rahoton ya nuna cewa an ɗauki matakin ne saboda matsayar da Xavi ya ɗauka dangane da zaɓukan da aka gudanar kwanan nan a kulob ɗin.

Majiyoyin labarin sun ce tsohon ɗan wasan ya nuna rashin jin daɗinsa kan matakin, bayan an sanar da shi cewa a halin yanzu ba a maraba da shi cikin ayyukan Barça Legends.

Sai dai Barcelona ta bayyana cewa lamarin na ɗan lokaci ne kawai, tana mai cewa akwai yiwuwar warware matsalar a nan gaba.

Wannan lamari ya jawo ce-ce-ku-ce tsakanin magoya bayan Barcelona, musamman ganin irin gagarumar gudunmawar da Xavi ya bayar ga kulob ɗin a matsayinsa na ɗaya daga cikin fitattun ’yan wasan da s**a taɓa bugawa ƙungiyar, kafin daga bisani ya zama kocinta.

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta nahiyar Turai (UEFA) ta sanar da naɗin alkalin wasa ɗan ƙasar Somaliya, Omar Abdulkadir Artan, d...
11/06/2026

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta nahiyar Turai (UEFA) ta sanar da naɗin alkalin wasa ɗan ƙasar Somaliya, Omar Abdulkadir Artan, domin jagorantar wasan ƙarshe na gasar UEFA Super Cup ta shekarar 2026.

Fabrizio Romano rawaito cewa UEFA ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar, inda ta ce an ɗauki matakin ne bayan tattaunawa da Hukumar Ƙwallon Ƙafar Afirka (CAF).

Za a fafata wasan ƙarshe na UEFA Super Cup ne a ranar 12 ga watan Agusta, 2026, tsakanin zakaran Gasar Zakarun Turai, Paris Saint-Germain, da kuma Aston Villa, wadda ta lashe gasar Europa League. Za a buga wasan a filin wasa na Salzburg Stadium da ke ƙasar Austria.

Naɗin Artan ya zo ne makonni kaɗan bayan ya shiga sahun alkalan wasa 52 da FIFA ta zaɓa domin gudanar da wasannin Gasar Kofin Duniya ta 2026.

Sai dai daga bisani hukumomin shige da fice na United States sun hana shi shiga ƙasar, lamarin da ya sa aka mayar da shi zuwa ƙasarsa ta Somalia tare da cire sunansa daga cikin jerin alkalan gasar.

Rahotanni sun nuna cewa bayan komawarsa gida, al’ummar Somaliya sun yi masa gagarumar tarba tare da nuna goyon baya gare shi. Artan ya gode musu kan wannan karamci, tare da bayyana cewa har yanzu yana da burin jagorantar wasanni a Gasar Kofin Duniya a nan gaba.

Masu bibiyar harkokin ƙwallon ƙafa na ganin cewa naɗin da UEFA ta yi wa Artan domin jagorantar ɗaya daga cikin manyan wasannin ƙwallon ƙafa a Turai wata alama ce ta amincewa da ƙwarewarsa da kuma ƙarfin gwiwar da yake da shi a fagen alkalancin wasa.

DA DUMI-DUMI: Majalisar wakilai ta amince da kudirin kafa ƴansandan jihohiMajalisar wakilai ta amince da kudirin gyaran ...
11/06/2026

DA DUMI-DUMI: Majalisar wakilai ta amince da kudirin kafa ƴansandan jihohi

Majalisar wakilai ta amince da kudirin gyaran kundin tsarin mulki da ke neman kafa rundunar ‘yansandan jihohi a Najeriya.

An amince da kudirin ne a zaman majalisar na ranar Alhamis bayan ‘yan majalisar sun kada kuri’ar amincewa da shi.

Amincewar da majalisar ta yi da kudirin na daga cikin muhimman matakan da ake dauka wajen sauya tsarin tsaro a kasar, inda jihohi za su samu damar kafawa da gudanar da rundunonin ‘yansandansu tare da hadin gwiwa da hukumomin tsaron tarayya.

Masu goyon bayan kudirin na ganin cewa kafa ‘yansandan jihohi zai taimaka wajen inganta tsaro da magance kalubalen rashin tsaro da ke addabar sassa daban-daban na kasar nan.

Sai dai kafin kudirin ya zama doka, har yanzu akwai wasu matakai na doka da kundin tsarin mulki da ya k**ata ya bi.

Ana ci gaba da samun saɓanin ra'ayi kan batun ficewar tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa A...
11/06/2026

Ana ci gaba da samun saɓanin ra'ayi kan batun ficewar tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, daga jam'iyyar APC a Jihar Gombe.

Daily Trust ta rawaito cewa yayin da ɓangaren Pantami ke cewa ya ajiye takardar murabus dinsa daga APC kafin ya koma PDP tare da samun tikitin takarar gwamna na jam'iyyar, wasu shugabannin APC na mazabarsa ta Pantami sun musanta cewa ya bi wannan tsari kafin sauya sheƙa.

Shugaban APC na Mazabar Pantami da ke Karamar Hukumar Gombe, Alhaji Bala Galda, ya shaida wa manema labarai cewa shi da kansa ne ya karɓi takardar murabus ɗin Pantami.

A cewarsa, takardar mai ɗauke da kwanan watan 19 ga Mayu, 2026, ta samu karɓuwa daga gare shi tare da sanya tambarin yatsa, yayin da mai bai wa APC shawara kan harkokin shari'a a mazabar, Malam Babangida Gololo, ya sanya hannu a matsayin shaida.

Galda ya bayyana cewa bayan Pantami ya shiga PDP kuma ya samu tikitin takarar gwamna, shugabannin APC na ƙaramar hukuma sun umarci shugabannin mazabar da kada su karɓi ko su sanya hannu a kowace takardar murabus da zai gabatar.

Sai dai ya ce ya sanar da su cewa ya riga ya karɓi takardar tun kafin wannan umarni, yana mai cewa babu wata doka da ta wajabta masa sanar da shugabannin jam'iyya a matakin ƙaramar hukuma ko jiha idan wani memba ya yanke shawarar ficewa daga jam'iyyar.

Ya kuma zargi shugabannin jam'iyyar da neman ya musanta karɓar takardar, amma ya ƙi amincewa da hakan saboda a cewarsa gaskiya ce da ba zai iya musantawa ba.

Shi ma Malam Babangida Gololo ya ce babu wani tanadi a kundin tsarin mulkin jam'iyyar da ya wajabta wa talakan memba gabatar da rubutacciyar takardar murabus kafin shiga wata jam'iyya, yana mai cewa a aikace, shiga sabuwar jam'iyya na nuna mutum ya fice daga tsohuwar jam'iyyarsa.

Sai dai Sakataren Yaɗa Labarai na APC a Jihar Gombe, Moses Kyari, ya ce jam'iyyar ta bukaci shugaban mazabar ya gabatar da kwafin takardar murabus ɗin da aka karɓa, amma bai yi hakan ba.

Kyari ya kuma bayyana cewa bisa tsarin jam'iyyar, sakataren mazaba ne ya k**ata ya karɓi irin wannan takarda ba shugaban mazaba ba.

Ya ƙara da cewa har yanzu sun gayyaci shugaban mazabar domin ya gabatar da asalin takardar ko ya bayyana a gaban jam'iyyar, amma bai amsa gayyatar ba.

A cewarsa, har yanzu sunan Pantami yana cikin rajistar mambobin APC da ke kan tsarin INEC, yana mai jaddada cewa jam'iyyar ba ta hana shi ficewa ba, amma tana ganin ya k**ata a bi ƙa'idar da ta dace wajen yin hakan.

Fadar White House ta kare matakin da gwamnatin Amurka ta ɗauka na hana alkalin wasa ɗan ƙasar Somaliya, Omar Abdulkadir ...
10/06/2026

Fadar White House ta kare matakin da gwamnatin Amurka ta ɗauka na hana alkalin wasa ɗan ƙasar Somaliya, Omar Abdulkadir Artan, shiga ƙasar, tana mai cewa an ɗauki matakin ne bisa dalilan tsaro.

Africa Trust ta rawaito cewa shahararren ɗan jaridar harkokin wasanni Fabrizio Romano, ya ambato rahoton jaridar The Athletic ta bayyana cewar White House ta bayyana cewa bayan ƙarin bincike da jami'an Hukumar Kwastam da Kare Iyakokin Amurka (CBP) s**a gudanar, an gano wasu bayanai da s**a haɗa da zargin alaƙa da wasu mutane da ake zargi da kasancewa mambobin ƙungiyoyin ta'addanci.

Sanarwar ta ce hakan ya sa Artan bai cancanci shiga Amurka ba bisa tanade-tanaden dokar shige da fice da zama ɗan ƙasa ta ƙasar.

Fadar White House ta jaddada cewa gwamnatin Donald Trump ba za ta amince da shigar duk wani mutum da ka iya zama barazana ga tsaron ƙasar ba.

Wannan na zuwa ne bayan rahotanni sun bayyana cewa an hana Artan shiga Amurka duk da kasancewarsa da ingantattun takardun tafiya da kuma bizar shiga ƙasar.

Lamarin ya janyo muhawara a tsakanin masu bibiyar harkokin wasanni da shige da fice, musamman ganin cewa Artan na fatan zama ɗan Somaliya na farko da zai yi alkalanci a gasar FIFA World Cup.

Rikice-rikicen jam’iyyun siyasa a Najeriya na ƙara k**ari bayan kammala zaɓen fidda gwani, yayin da INEC ta sanya wa’adi...
10/06/2026

Rikice-rikicen jam’iyyun siyasa a Najeriya na ƙara k**ari bayan kammala zaɓen fidda gwani, yayin da INEC ta sanya wa’adin 11 ga watan Yuli a matsayin ranar miƙa sunayen ’yan takarar zaɓen 2027.

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya (INEC) ta sanya ranar 26 ga watan Yuni, 2026 domin bai wa jam’iyyun siyasa lambobin shiga tsarin na’urar mika bayanan ’yan takara, tare da ayyana ranar 11 ga watan Yuli a matsayin wa’adin ƙarshe na gabatar da sunayen ’yan takara domin babban zaɓen shekarar 2027.

Jaridar punch ta rawaito cewa matakin na zuwa ne yayin da wasu jam’iyyun siyasa ke ci gaba da kokarin warware rikice-rikicen da s**a biyo bayan zaben fidda gwani, da kuma kammala shirye-shiryen tantance ’yan takararsu.

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ne ya bayyana hakan a Abuja yayin taron tuntuba na biyu na wannan shekara da shugabannin jam’iyyun siyasa.

Ya ce daga ranar 27 ga watan Yuni ne jam’iyyu za su fara amfani da tsarin na’urar mika bayanan ’yan takara, inda aka tanadi ranar 11 ga watan Yuli a matsayin wa’adin ƙarshe na kammala aikin.

Amupitan ya bayyana cewa lambobin shiga tsarin za a bai wa jami’an ƙasa na jam’iyyu domin su dora sunaye, bayanan sirri da sauran takardun da ake buƙata na ’yan takara.

Ya kuma gargadi jam’iyyun siyasa da su tabbatar da cewa ma’aikatan fasahar sadarwa da sauran jami’ansu sun shirya tsaf domin kauce wa matsalolin da ka iya tasowa kafin cikar wa’adin.

Shugaban na INEC ya nuna damuwa kan yadda rikice-rikicen cikin gida da shari’o’in da s**a shafi shugabancin wasu jam’iyyu ke ci gaba da yawaita, yana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga shirye-shiryen gudanar da zaɓen 2027.

Ya jaddada cewa INEC za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta cikin adalci da bin tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokokin zaɓe.

A cewarsa, duk da karar da INEC ta daukaka kan wasu hukunce-hukuncen kotu da s**a shafi jadawalin zaɓe, hukumar za ta ci gaba da aiwatar da shirye-shiryenta k**ar yadda doka ta tanada.

Rahotanni sun nuna cewa jam’iyyu irin su ADC, YPP, APGA, SDP, LP da NDC sun bayyana shirinsu na mika sunayen ’yan takararsu ga INEC kafin cikar wa’adin da aka sanya.

Haka kuma, wasu daga cikin jam’iyyun na ci gaba da tuntubar juna kan batun zaɓen mataimakan ’yan takarar shugaban ƙasa, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

10/06/2026

Rikice-rikicen jam’iyyun siyasa a Najeriya na ƙara k**ari bayan kammala zaɓen fidda gwani, yayin da INEC ta sanya wa’adin 11 ga watan Yuli a matsayin ranar miƙa sunayen ’yan takarar zaɓen 2027

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya (INEC) da ta dawo da tsarin raji...
10/06/2026

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya (INEC) da ta dawo da tsarin rajistar jam’iyyar Access Party tare da ba ta lambar shiga (Access Code) domin kammala rajistarta a matsayin jam’iyyar siyasa a Najeriya.

Daily Nigerian ta rawaito cewa hukuncin ya biyo bayan ƙarar da shugaban riƙo na jam’iyyar, Audu Bulama-Bukarti, da Mevon Samuel s**a shigar a gaban kotu, bayan INEC ta dakatar da rajistar jam’iyyar saboda tambarin da ta gabatar.

A hukuncin da ya yanke ranar Laraba, Mai Shari’a Obiora Atuegwu Egwuatu ya bayyana cewa matakin da INEC ta ɗauka na dakatar da rajistar jam’iyyar bisa hujjar rashin dacewar tambarinta ya saɓa wa doka.

Kotun ta ce wasiƙar da INEC ta fitar tana cin karo da tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 da kuma Dokar Zaɓe ta 2022.

Mai shari’ar ya kuma tabbatar da cewa tambarin da Access Party ta gabatar ya dace da doka, kuma bai yi k**a da wata tambarin da za ta hana a yi mata rajista ba.

Kotun ta soke wasiƙar dakatarwar da INEC ta aika wa jam’iyyar, tare da umartar hukumar da ta dawo da tsarin rajistar Access Party tare da ba ta damar cike fom ɗin rajista da miƙa sauran takardun da ake buƙata haka kuma, kotun ta ci tarar INEC kuɗi har Naira 500,000.

Da yake martani ga hukuncin, Bulama-Bukarti ya bayyana shi a matsayin nasara ga dimokuraɗiyyar Najeriya da kuma haƙƙin ‘yan ƙasa na kafa jam’iyyun siyasa.

Ya kuma yi kira ga INEC da ta gaggauta aiwatar da umarnin kotun domin bai wa jam’iyyar damar kammala rajistarta kafin zaɓukan shekarar 2027.

A nasa ɓangaren, lauyan masu ƙarar, Jude Akpevweoghene-Daniel, ya ce hukuncin ya sake jaddada cewa dukkan hukumomin gwamnati dole ne su yi aiki cikin iyakokin doka da adalci.

Masu sa ido kan harkokin siyasa na ganin cewa hukuncin na iya yin tasiri wajen yadda INEC za ta rika kula da buƙatun rajistar sabbin jam’iyyun siyasa yayin da ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

Address

Kano

Telephone

+2348177352017

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Africa Trust posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Africa Trust:

Share