Kadial News

Kadial News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Kadial News, Kano.

HOTUNA: Yadda aka yi jana'izar Birgediya-Janar Braimah da sauran sojojin da ƴan Boko Haram su ka kashe a Borno
15/04/2026

HOTUNA: Yadda aka yi jana'izar Birgediya-Janar Braimah da sauran sojojin da ƴan Boko Haram su ka kashe a Borno

Gwamnatin Tarayya ta gyara tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon ministan shari'a Abubakar Malami, inda ta cire zargin ɗauk...
15/04/2026

Gwamnatin Tarayya ta gyara tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon ministan shari'a Abubakar Malami, inda ta cire zargin ɗaukar nauyin ta’addanci, ta maye gurbin sa da zargin mallakar mak**ai ba bisa ka’ida ba.

A yayin zaman kotun, Malami da ɗansa sun musanta sabon zargin, yayin da alkalin, Joyce Abdulmalik, ta ba su damar ci gaba da zama a beli.

An ɗage shari’ar zuwa ranar 26 ga Mayu da 15 ga Yuni domin ci gaba da sauraro.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta ayyana yaƙin “ba sani ba sabo” kan cin hanci da rashawa, inda ta gargaɗi jami’anta ...
15/04/2026

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta ayyana yaƙin “ba sani ba sabo” kan cin hanci da rashawa, inda ta gargaɗi jami’anta da ke kan hanyoyi cewa duk wanda aka k**a da laifi zai yaba wa aya zaƙinta.

Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗin cewa ambaliya za ta shafi jihohi da dama a Najeriya, ciki har da Bayelsa, Delta, Adamaw...
15/04/2026

Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗin cewa ambaliya za ta shafi jihohi da dama a Najeriya, ciki har da Bayelsa, Delta, Adamawa da Kebbi, a shekarar 2026.

Rahoton ya nuna cewa dubban al’ummomi a jihohi 33 da Abuja na cikin haɗarin ambaliya mai tsanani, yayin da wasu da dama za su fuskanci matsakaici ko ƙananan haɗari.

Haka kuma, an yi hasashen ambaliya a manyan birane k**ar Kano, Lagos da Abuja sak**akon ruwan sama mai yawa da matsalolin magudanan ruwa, tare da yiwuwar ambaliyar teku a jihohin bakin ruwa.

Gwamnati ta bukaci jihohi, ƙananan hukumomi da al’umma su fara shiri tun yanzu domin rage illar ambaliyar.

06/04/2026
Hukumomin rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) sun tabbatar da mutuwar babban jami’in leƙen asirin su, Majid Khademi, b...
06/04/2026

Hukumomin rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) sun tabbatar da mutuwar babban jami’in leƙen asirin su, Majid Khademi, bayan wani hari ta sama da aka kai masa a safiyar yau.

A cewar wata sanarwa da aka wallafa ta kafar labarai ta Tasnim, Khademi ya rasu ne sak**akon harin da ya afka masa, duk da cewa ba a bayyana cikakken bayani kan wurin da lamarin ya faru ba.

Rahotanni sun nuna cewa marigayin ya rike muhimman muk**ai guda biyu a cikin IRGC, inda ya kasance shugaban sashen kare bayanan sirri (Intelligence Protection Organization) da kuma jagoran sashen leƙen asiri (Intelligence Organization) na rundunar.

Har zuwa yanzu dai babu wata sanarwa daga Isra'ila dangane da zargin hannu a harin, lamarin da ke ƙara jefa tambayoyi kan wanda ke da alhakin kai wannan farmaki.

Mutuwar Khademi na zuwa ne a wani lokaci da ake ci gaba da fuskantar tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya, inda hare-hare da martani ke ci gaba da ƙara k**ari tsakanin ƙasashe Amurka-Israila da Iran.

Wasu ‘yan ta’adda sun kai hari a ƙauyen Ariko da ke ƙaramar hukumar Kachia a Jihar Kaduna, inda s**a kai farmaki kan maj...
05/04/2026

Wasu ‘yan ta’adda sun kai hari a ƙauyen Ariko da ke ƙaramar hukumar Kachia a Jihar Kaduna, inda s**a kai farmaki kan majami’u biyu a yayin bikin Easter, s**a kashe aƙalla mutane bakwai tare da sace wasu da dama.

Rahotanni sun nuna cewa harin ya faru ne da safiyar ranar Lahadi, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin firgici da tashin hankali.

Dan majalisar yankin Awon Ward, Mark Bawa, ya tabbatar da faruwar lamarin ta wayar tarho, inda ya ce majami’un da abin ya shafa sun haɗa da First ECWA Church da kuma St. Augustine Catholic Church da ke Ariko.

Ya ce har yanzu ana tattara cikakken bayani kan adadin waɗanda s**a mutu, domin wasu rahotanni na cewa mutum bakwai ne s**a rasu, yayin da wasu ke cewa sun kai takwas.

A lokacin da aka tuntubi jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya ce za su fitar da cikakken bayani kan lamarin nan gaba.

Ƙungiyar likitoci masu neman kwarewa ta sanar da shiga yajin aikin sai baba-ta-gani a faɗin Najeriya daga ranar 7 ga Afr...
05/04/2026

Ƙungiyar likitoci masu neman kwarewa ta sanar da shiga yajin aikin sai baba-ta-gani a faɗin Najeriya daga ranar 7 ga Afrilu, 2026 k**ar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kebbi, sun kashe ‘yan ta’addan Lakurawa da s**a kai hari Ƙaramar Hukumar Dandi.
05/04/2026

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kebbi, sun kashe ‘yan ta’addan Lakurawa da s**a kai hari Ƙaramar Hukumar Dandi.

HOTUNA: Yadda tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli na jihar kano Hon. Dr. Kabiru Ibrahim Getso, Ya kai ziyara...
05/04/2026

HOTUNA: Yadda tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli na jihar kano Hon. Dr. Kabiru Ibrahim Getso, Ya kai ziyara karamar hukumar sa ta Gwarzo domin yin gaishe-gaishe, ta'aziyya, da duba marasa lafiya.

📸 Aliyu Abdul Garo

An sake samun wani sabon hari a Jihar Plateau inda aka kashe aƙalla mutum uku, ƙasa da sa’o’i 24 bayan ziyarar Shugaban ...
05/04/2026

An sake samun wani sabon hari a Jihar Plateau inda aka kashe aƙalla mutum uku, ƙasa da sa’o’i 24 bayan ziyarar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, zuwa jihar domin jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe a baya.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun kai farmaki ne a yankin Nyango Gyel da ke ƙaramar hukumar Jos ta Kudu a daren Juma’a, inda s**a fara harbe-harbe ba tare da kakkautawa ba kafin daga bisani su tsere.

Majiyoyi sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:40 na dare, lamarin da ya haddasa fargaba a tsakanin mazauna yankin.

Sakataren ƙungiyar matasan Berom, Rwang Tengwong, ya tabbatar da aukuwar harin, yana mai bayyana shi a matsayin rashin hankali da cin zarafin fararen hula marasa laifi.

Wani sabon rahoto da ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Human Rights Watch ta fitar ya bayyana cewa dakarun ƙasar Burkina...
05/04/2026

Wani sabon rahoto da ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Human Rights Watch ta fitar ya bayyana cewa dakarun ƙasar Burkina Faso sun kashe fararen hula fiye da yadda ƙungiyoyin ‘yan ta’adda s**a yi a cikin shekaru biyu da s**a gabata.

Rahoton ya nuna cewa daga watan Janairun 2023 zuwa Afrilun 2025, sojojin Burkina Faso tare da ƙungiyar sa-kai ta masu kare ƙasa (VDP) sun kashe akalla fararen hula 1,255, ciki har da yara 193.

Rahoton ya kuma nuna cewa a daidai wannan lokaci, ƙungiyar JNIM ta kashe fararen hula 582, ciki har da yara 15 adadin da ya ragu da kusan kashi 73 cikin ɗari idan aka kwatanta da wanda ake dangantawa da sojojin ƙasar.

Address

Kano

Telephone

+2348062237474

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kadial News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kadial News:

Share