22/06/2026
DUMI-DUMI: Sojoji Sun hallaka wasu 'Yan Ta'adda Biyu A jihar Sokoto! 🔥🇳🇬
Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sake samun gagarumar nasara a yaƙin da suke yi da 'yan ta'adda a yankin Arewa maso Yamma.
Rahotanni sun bayyana cewa dakarun sun dakile wani yunƙurin harin 'yan ta'adda a Tureta, Jihar Sokoto, inda s**a fatattake su kafin su cimma manufarsu.
Bayan haka, sojojin sun bi sahun maharan har zuwa Sulubawa Gidan Kare, inda s**a yi artabu da su tare da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, sannan s**a kwato shanu da aka sace da kuma babura biyu da 'yan ta'addan ke amfani da su.
A wani samame da aka kai da asubahin yau a ƙaramar hukumar Matazu, Jihar Katsina, sojojin sun kashe 'yan ta'adda biyu, yayin da wasu da dama s**a tsere da raunukan harbin bindiga.
An kuma ƙwato:✅ Bindigar PKT guda 1✅ Bindigar AK-47 guda 1 tare da alburusai✅ Babura guda 3✅ Wayoyin sadarwa✅ Dabbobin da aka sace da sauran kayayyakin aiki.
Hukumar sojin ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da kai farmaki kan maboyar 'yan ta'adda har sai an tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Me kuke ganin ya k**ata gwamnati ta ƙara yi domin kawo ƙarshen ta'addanci a Arewa maso Yamma?