G.M.C HAUSA

G.M.C HAUSA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from G.M.C HAUSA, Social Media Agency, Kano.

Kayi Following GMC HAUSA Domin samun labarai da dumi dumi kuma Sahihai ingantattun Wanda Suka shafi Tsaro, Tattalin arziki, da Kuma siyasa

A Koda wanne lokaci.

DUMI-DUMI:  Sojoji Sun hallaka wasu 'Yan Ta'adda Biyu A jihar  Sokoto! 🔥🇳🇬Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sake samun ...
22/06/2026

DUMI-DUMI: Sojoji Sun hallaka wasu 'Yan Ta'adda Biyu A jihar Sokoto! 🔥🇳🇬

Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun sake samun gagarumar nasara a yaƙin da suke yi da 'yan ta'adda a yankin Arewa maso Yamma.

Rahotanni sun bayyana cewa dakarun sun dakile wani yunƙurin harin 'yan ta'adda a Tureta, Jihar Sokoto, inda s**a fatattake su kafin su cimma manufarsu.

Bayan haka, sojojin sun bi sahun maharan har zuwa Sulubawa Gidan Kare, inda s**a yi artabu da su tare da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, sannan s**a kwato shanu da aka sace da kuma babura biyu da 'yan ta'addan ke amfani da su.

A wani samame da aka kai da asubahin yau a ƙaramar hukumar Matazu, Jihar Katsina, sojojin sun kashe 'yan ta'adda biyu, yayin da wasu da dama s**a tsere da raunukan harbin bindiga.

An kuma ƙwato:✅ Bindigar PKT guda 1✅ Bindigar AK-47 guda 1 tare da alburusai✅ Babura guda 3✅ Wayoyin sadarwa✅ Dabbobin da aka sace da sauran kayayyakin aiki.

Hukumar sojin ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da kai farmaki kan maboyar 'yan ta'adda har sai an tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Me kuke ganin ya k**ata gwamnati ta ƙara yi domin kawo ƙarshen ta'addanci a Arewa maso Yamma?

😭 ALLAHU AKBAR! WANNAN ABIN TAKAICI NE! 😭A gaban su aka kashe mahaifiyarsu... sannan aka ƙona gawarta! 💔Waɗannan su ne '...
22/06/2026

😭 ALLAHU AKBAR! WANNAN ABIN TAKAICI NE! 😭
A gaban su aka kashe mahaifiyarsu... sannan aka ƙona gawarta! 💔

Waɗannan su ne 'ya'yan Malama Ummul Khairi, malamar Islamiyyar da wasu matasa s**a yi wa kisan gilla tare da ƙona gawarta bisa zargin satar yara—zargin da har zuwa wannan lokaci babu wata hujja da aka tabbatar da ita.

Lamarin ya jefa iyali da al'umma cikin jimami, yayin da ake kira ga hukumomi su tabbatar da adalci tare da hukunta duk wanda aka samu da hannu a wannan mummunan ta'asa.

Allah Ya jikanta da rahama, Ya ba iyalanta haƙurin jure wannan babban rashi. Amin. 🤲🕊️

😭 ALLAH SARKI! RASHIN IMANI😭An k**a wata mata a jihar Anambra bisa zargin yi wa ƙaramin ɗan aikinta azaba ta rashin iman...
22/06/2026

😭 ALLAH SARKI! RASHIN IMANI😭

An k**a wata mata a jihar Anambra bisa zargin yi wa ƙaramin ɗan aikinta azaba ta rashin imani.

Rahotanni sun ce ana zargin matar da kona wuƙa tare da danna ta a jikin yaron, lamarin da ya haddasa masa munanan raunuka har fatar jikinsa ta sale.

Bayan samun rahoton abin da ake zargin ya faru, mazauna yankin da makwabta sun kewaye matar kafin jami'an tsaro su k**a ta domin ci gaba da bincike.
Wane hukunci kuke ganin ya k**ata a ɗauka kan duk wanda aka samu da laifin cin zarafin yara irin wannan? Ku bayyana ra'ayinku. 👇

🚨 LABARI MAI TAYAR DA HANKALI! 😳Lakurawa Sun Mamaye Wani gari a Jihar Neja, Dan yin Wa'azi ga Mazauna Yankin Kan Tsattsa...
22/06/2026

🚨 LABARI MAI TAYAR DA HANKALI! 😳

Lakurawa Sun Mamaye Wani gari a Jihar Neja, Dan yin Wa'azi ga Mazauna Yankin Kan Tsattsauran Ra'ayi

Rahotanni sun bayyana cewa wasu 'yan ta'adda da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne, ɗauke da muggan mak**ai, sun kutsa cikin ƙauyen Zugurma da ke ƙaramar hukumar Mashegu a Jihar Neja a ranar Lahadi.
Bayan sun shiga ƙauyen, an ce sun tara mazauna yankin wuri guda, inda s**a yi musu wa'azi tare da yaɗa akidu da ra'ayoyin tsattsauran ra'ayi.
An bayyana cewa ƙauyen Zugurma na kusa da dajin Kainji Lake National Park, yankin da ke fama da matsalolin tsaro a lokuta daban-daban.
⚠️ Har yanzu jami'an tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan lamarin ba.
Allah Ya Kare Najeriya, Ya ba jami'an tsaro nasara, Ya tabbatar da zaman lafiya a ƙasarmu. 🤲🇳🇬

😭 ABIN TAUSAYI! 😭 An Hallaka Wata  Malamar Islamiyya Bayan An Yi Mata Zargin Satar Yara a Zariya.Rahotanni sun bayyana c...
21/06/2026

😭 ABIN TAUSAYI! 😭 An Hallaka Wata Malamar Islamiyya Bayan An Yi Mata Zargin Satar Yara a Zariya.

Rahotanni sun bayyana cewa wata Malamar Islamiyya mai suna Ummulkhairi ta rasa ranta a yankin Mararaban Jos da ke Zariya bayan wasu fusatattun matasa sun zarge ta da satar yara.

An ce bayan an kai ta ofishin 'yan sanda domin gudanar da bincike, lamarin ya rikice, inda aka yi ikirarin cewa wasu fusatattun matasa s**a fito da ita tare da kashe ta sannan s**a ƙona gawarta da babur ɗin wani da ya je domin ba da shaida a kanta.

Rahotanni sun ce marigayiyar uwa ce mai 'ya'ya sama da biyar, kuma ta je yankin ne domin halartar wani taron wa'azi.

lamarin ya tayar da hankali matuƙa, kuma ya sake jawo kira ga jama'a da su guji ɗaukar doka a hannunsu tare da bai wa hukumomi damar gudanar da bincike kafin yanke hukunci.

Allah Ya gafarta wa Malama Ummulkhairi, Ya ba iyalanta da masoyanta haƙurin jure wannan babban rashi. 🤲💔
Me kuke gani kan wannan lamari? Ku bayyana ra'ayoyinku cikin mutunci.

21/06/2026

🚨 NAJERIYA KENAN? 😭

Bello Turji ya wallafa bidiyo, yana ikirarin cewa mayakansa sun yi nasara a kan dakarun sojojin Najeriya.

A cikin bidiyon da ya bazu a kafafen sada zumunta, Bello Turji ya yi ikirarin cewa mayakansa sun yi galaba a wani artabu da dakarun sojojin Najeriya.

⚠️ Sai dai har zuwa yanzu, ba a samu wata sanarwa daga rundunar sojin Najeriya da ta tabbatar da wannan ikirari ba.

🤔 Me kuke gani kan wannan ikirari? Ku bayyana ra'ayoyinku a sashin sharhi.

21/06/2026

🚨 NAJERIYA KENAN? 😭

Bello Turji ya wallafa bidiyo, yana ikirarin cewa mayakansa sun yi nasara a kan dakarun sojojin Najeriya.

A cikin bidiyon da ya bazu a kafafen sada zumunta, Bello Turji ya yi ikirarin cewa mayakansa sun yi galaba a wani artabu da dakarun sojojin Najeriya.

⚠️ Sai dai har zuwa yanzu, ba a samu wata sanarwa daga rundunar sojin Najeriya da ta tabbatar da wannan ikirari ba.
🤔 Me kuke gani kan wannan ikirari? Ku bayyana ra'ayoyinku a sashin sharhi.

🚨 INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN! 😭Yanzu Yanzu 'Yan bindiga sun kashe tsohuwar ma'aikaciyar gidan talabijin na Jiha...
21/06/2026

🚨 INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN! 😭

Yanzu Yanzu 'Yan bindiga sun kashe tsohuwar ma'aikaciyar gidan talabijin na Jihar Ogun.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu 'yan bindiga sun kai hari a yankin Agodo, inda s**a kashe tsohuwar ma'aikaciyar gidan talabijin na Jihar Ogun, Kitan Oyesiku, tare da jami'in tsaronta.

Jaridar Punch Newspapers ta rawaito cewa Rundunar 'yan sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, tare da bayyana cewa an fara bincike domin gano waɗanda s**a aikata wannan mummunan hari.

😢 Allah Ya jikansu da rahama, Ya ba iyalansu da masoyansu haƙurin jure wannan babban rashi.

🚨 DUMI-DUMI: BELLO TURJI NA HORAS DA MAYAKAN SA ANA DABARUN AMFANI DA MAKAMAI NA ZAMANI  A SOKOTO! 😳Rahotanni sun ce ana...
21/06/2026

🚨 DUMI-DUMI: BELLO TURJI NA HORAS DA MAYAKAN SA ANA DABARUN AMFANI DA MAKAMAI NA ZAMANI A SOKOTO! 😳

Rahotanni sun ce ana zargin mayakan Bello Turji da gudanar da atisayen soja da horon amfani da sabbin mak**ai a wasu yankunan gabashin jihar Sokoto da ke kan iyaka da Zamfara.

An kuma yi zargin cewa mayakan na samun horo kan amfani da na'urorin hangen dare tare da shirin ƙara ƙarfafa ƙungiyarsu kafin damina ta tsananta.

Sai dai har zuwa wannan lokaci, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba, kuma ba a tabbatar da waɗannan zarge-zarge daga majiyoyi masu zaman kansu ba.
🤔 Me kuke ganin ya k**ata gwamnati da hukumomin tsaro su yi kan wannan rahoto? Ku bayyana ra'ayoyinku a sashin sharhi.

🚨 DUMI-DUMI: MUTANE SUN SHEKE WANI DA AKE ZARGIN MAI BAI WA 'YAN BINDIGA BAYANAI A JIHAR ZAMFARA 😳Rahotanni sun ce fusat...
20/06/2026

🚨 DUMI-DUMI: MUTANE SUN SHEKE WANI DA AKE ZARGIN MAI BAI WA 'YAN BINDIGA BAYANAI A JIHAR ZAMFARA 😳

Rahotanni sun ce fusatattun mazauna garin Gummi da ke jihar Zamfara sun kashe wani mutum da ake zargi da bai wa 'yan bindiga bayanai.

Sai dai har yanzu ba a tabbatar da cikakken bayani daga hukumomin tsaro ba kan lamarin, kuma ba a yanke hukunci a kansa a gaban kotu ba kafin aukuwar wannan lamari.

❓Shin kuna ganin ya dace al'umma su ɗauki doka a hannunsu idan suna zargin wani da aikata laifi, ko kuwa ya k**ata a miƙa shi ga hukumomin tsaro domin a gudanar da bincike? Ku bayyana ra'ayoyinku a sashin sharhi.

Address

Kano

Telephone

+2347068973897

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when G.M.C HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share