ALAQA web series

REMAIN Cristiano Ronaldo Insha Allah
19/08/2026

REMAIN Cristiano Ronaldo Insha Allah

Yadda ka ƙuntata mana, Allah Ya ƙuntata maka Tinubu😌 amin
17/08/2026

Yadda ka ƙuntata mana, Allah Ya ƙuntata maka Tinubu😌 amin

ALHAMDULILLAH Yanzu haka dan uwanmu Sulaiman Sherah Danwawu ya koma cikin iyalanshi lafiya bayan kotu ta bada belinshi. ...
17/08/2026

ALHAMDULILLAH Yanzu haka dan uwanmu Sulaiman Sherah Danwawu ya koma cikin iyalanshi lafiya bayan kotu ta bada belinshi.

An zalunce shi an cutar dashi an tsare shi har na tsawon kwanaki 11 saboda kawai bambancin ra'ayin siyasa na fadin albarkacin baki.

Tun ranar da aka kai Suleiman Shera Danwawu kotu, Alkali yaga karar shirrita ce yana kokarin ya bada belin shi aka kira waya aka mishi barazana daga farin gida haka dole ya hana belinshi sai yau Litinin.

Wallahi kusan duk matasan gidan Pantamiyya da yawansu an kirasu an musu barazanar kamu, wasu an k**a su Allah ya kubutar dasu wasu an kulla musu sharruka iri-iri Allah ya kubutar dasu. Kunsan me yasa suke yi mana haka? Wallahi don mu tsorita mu daina goyon bayan maigidanmu Professor Isa Ali Pantami mu koma gefe muyi shiru a cuci talakawan jihar Gombe.

Wallahi tallahi ku sani kamu da dauri baya bamu tsoro ko kadan hasalima kwarin gwiwa yake kara mana. Kuma duk wanda yake bibiyar siyasar tafiyar Pantamiyya yasanmu da bin doka da oda, in kaga mun taba wani to shi ya taba mu. Kuma wallahi baku isa ku hanamu fadan Albarkacin bakinmu ba, domin dokar kasa ta bawa kowa damar fadan ra'ayin shi.

A siyasance duk wanda yayi maka cin mutuncin da ya wuce siyasa muna goyon kakai shi kara domin a ladantar dashi amma irin wannan na Suleiman Shera Danwawu wallahi kowa yasan zallar zalunci ne sai-dai son zuciya ta hana a fada.

Akwai matasa da yawa a Gombe da s**a ci mutuncin mutane wanda ya wuce siyasa kuma mun goyi bayan a dauki matakin shari'a akansu a kowane gida suke, ta hakan ne kadai za'a tsaftace harkar siyasa a Gombe.

A DAWAR SIYASA DABAN
CIN MUTUNCI DABAN

Ai fa Yan Siyasa Arewacin Nigeria lokaci yayi an fara hito da Kudade ana Rabawa Talakawa Shekara 3 suna Cikin halin da s...
17/08/2026

Ai fa Yan Siyasa Arewacin Nigeria lokaci yayi an fara hito da Kudade ana Rabawa Talakawa Shekara 3 suna Cikin halin da suke ciki duk Ba'a wai waye su ba sai Yanzu da akaga Lakocin Amfani su yazo.

Wasu yanku nan ma Babu Ruwa ba Wuta ba Tsaro Kullum ana sace su babu wanda ya taba Zuwa sai Yanzu to Wlh Jama'a ku Farka duk Wanda ya baku ku amsa dama hakinku ne amma Ranar Zabe ku Zabi Nagari ba Bata gari ba.

Mutanin Osun sun karbi kudi da buhun shinkafa, kuma sun ki zabe APC toh gane GA wane
17/08/2026

Mutanin Osun sun karbi kudi da buhun shinkafa, kuma sun ki zabe APC toh gane GA wane

NA TAUSAYAWA  MUSA MAISANA: WATAKILA BAI FAHIMCI INDA YA SHIGO BA 😔Abin da ya faru da jarumi  Musa Maisana a Katsina abi...
17/08/2026

NA TAUSAYAWA MUSA MAISANA: WATAKILA BAI FAHIMCI INDA YA SHIGO BA 😔

Abin da ya faru da jarumi Musa Maisana a Katsina abin tausayi ne, kuma gaskiya akwai darasin da ya k**ata a koya daga lamarin.

Ba wai rainin wayo ba ne ga Maisana, amma a ganina bai fahimci irin yanayin da yake shiga ba. Katsinawa da al’ummar yankin sun dade suna bayyana matsalolinsu da irin abubuwan da suke fuskanta, don haka zuwa tsaye a tsakiyar jama’a domin isar da saƙon siyasa da ba su amince da shi ba, musamman a irin wannan yanayi, abu ne da zai iya haifar da tashin hankali.

Wallahi idan ba ka san yanayin gari ba, ba ka tashi ka hau ganuwar garinsu kana musu abin da zai fusata su ba. 😔

Musa Maisana jarumi ne, kuma ya k**ata a kare rayuwarsa k**ar yadda ake kare rayuwar kowa. Amma shi ma wannan lamari ya zama darasi gare shi da sauran masu shiga harkar wayar da kai:

Ba kowane wuri ne ya dace a je da irin saƙo guda ba.

Allah Ya kiyaye gaba, Ya ba kowa hikimar sanin lokacin magana, lokacin yin shiru, da kuma lokacin janye wa domin kare kai.

Katsinawa ma Allah Ya kyauta—fushi bai k**ata yakai ga bugu ba 🤲

Shugaban Matasan Jam’iyar APC Ya Ce Rawar Adeleke Ta Taimaka Masa a OsunShugaban Matasan Jam’iyar APC na ƙasa, Dayo Isra...
17/08/2026

Shugaban Matasan Jam’iyar APC Ya Ce Rawar Adeleke Ta Taimaka Masa a Osun

Shugaban Matasan Jam’iyar APC na ƙasa, Dayo Israel, ya ce rawar da Gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ke yi da kuma kusancinsa da jama’a sun taimaka masa wajen samun karɓuwa a zaɓen gwamnan jihar.

Ya ce iya rawa, waƙa da mu’amala da jama’a sun ƙarfafa alaƙar Adeleke da masu zaɓe, yana mai cewa siyasa ba ta tsaya kan manufofi kaɗai ba, har da motsin zuciya da kusanci da jama’a.

Israel ya kuma yaba wa mawaki Davido kan rawar da ya taka wajen jawo matasa da amfani da tasirinsa da kafafen sada zumunta wajen tallafa wa yaƙin neman zaɓen Adeleke.

Ya bukaci APC ta koyi darasi daga rashin nasarar da ta samu a Osun, ta ƙarfafa tsarin jam’iyyar a ƙasa, warware rikice-rikicen cikin gida da kuma ƙara bai wa matasa da mata muhimmanci gabanin zaɓen 2027.

ALLAHU AKBAR: Dattijuwa Mai Shekaru 81 Ta Sauke Alƙur’ani Mai Girma a KanoHajiya Sa’adatu Nuhu Waziri, mai shekaru 81, t...
17/08/2026

ALLAHU AKBAR: Dattijuwa Mai Shekaru 81 Ta Sauke Alƙur’ani Mai Girma a Kano

Hajiya Sa’adatu Nuhu Waziri, mai shekaru 81, ta sauke Alƙur’ani mai girma a unguwar Tudun Wazirchi, Kano, bayan shafe kusan shekaru 30 zuwa 40 tana karatun Alƙur’ani.

An gudanar da bikin saukar a jiya Lahadi, 16 ga Agusta 2026, inda ’ya’yanta da jikokinta s**a taru domin taya ta murna tare da gudanar da addu’o’i.

Allah Ya ƙara mata lafiya, Ya sanya Alƙur’ani ya zama haske da albarka a rayuwarta. Amin.

Ana ci gaba da aikin gina Kano Northern Bypass, wata muhimmiyar hanyar da ta kai kusan kilomita 38, wadda za ta haɗa han...
17/08/2026

Ana ci gaba da aikin gina Kano Northern Bypass, wata muhimmiyar hanyar da ta kai kusan kilomita 38, wadda za ta haɗa hanyar Kano–Hadejia da hanyar Kano–Katsina.

Ana sa ran kammala aikin zai taimaka wajen rage cunkoson ababen hawa a cikin birnin Kano, musamman manyan motoci da ke ratsa cikin birnin daga yankin Arewa maso Gabas zuwa Arewa maso Yamma. Hakan kuma zai rage lokacin zirga-zirga da kuma sauƙaƙa jigilar kayayyaki.

Aikin na daga cikin manyan ayyukan samar da ababen more rayuwa da Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa, ƙarƙashin kulawar Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya, wadda Minista David Umahi ke jagoranta.

A cewar bayanan Ma’aikatar Ayyuka, aikin yana ƙunshe da manyan gine-ginen gada guda 10, tare da wasu muhimman abubuwan more rayuwa da za su inganta zirga-zirga da haɗin kan hanyoyin sufuri a Kano

Duk Wanda Yake Tunanin Na Daina Mauludi, To Yanzu Ma Na Fara, Inji Abubakar Ɗan GaskeAlhaji Abubakar Ɗan Gaske ya bayyan...
17/08/2026

Duk Wanda Yake Tunanin Na Daina Mauludi, To Yanzu Ma Na Fara, Inji Abubakar Ɗan Gaske

Alhaji Abubakar Ɗan Gaske ya bayyana hakan ne a wajen wani taron hidimtawa Annabi SAW da hamshaƙin ɗan kasuwa a Kano, Sani Kwangila Yakasai (SKY) ya shirya.

A kwanakin baya ne dai aka dinga yaɗa cewa Ɗan Gaske ya daina maulidin da yaje shirya duk shekara saboda wani furici da ya yi na cewa Ahlussunnah masoya Annabi SAW ne.

Alhaji Abubakar Ɗan Gaske ya ƙara da cewa janyewa daga cikin wata hidima ta Manzon Allah SAW tamkar ya yi riđđa ne a wajensa, k**ar yadda Rariya ta ci karo da bayanan nasa a wani bidiyo.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ALAQA web series posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share