24/09/2024
Bafa wai lallaɓa SLS muke akan ya cire kafet ɗin nan ba, abune da ya zama dole sai ya cire shi, bama buƙatar bamu hujja akai, idan har ba komai bane ka rubuta sunan tsohon ka a ƙasa amma ba namu Annabin ba, kuma k**a daina zaton wai sunan ka ka rubuta ba sunan ka bane ara kai, dan haka mu bama takai muke ba, ko ba'a takawa babu ladabi a ciki b***e kowa yasan anyi kafet ne dan a shimfiɗa kuma a taka shi.
Babu ruwan mu da sabgar ka, amma anan kan damu kake, bisa kyautata zato dama mun san ba da niyya kai ba tunda kai musulmi ne kuma kana son Manzan Allah, amma daga lokacin da masoya s**a ja hankali a kan wannan kuskuren muka fahimci akwai karancin sanin waye Annabi AlayHis Sallam tare da kai tunda ka tsaya bada hujja akan abinda kai kuma kake so ka nuna ba kuskure bane bayan shine mafi girman kuskure a wajen mu dama duk musulmai baki ɗaya.
Khalifa Habeebu Rasulullah II