08/02/2026
Allahu Akbar 😭
Tabbas jiya nayi mafarkin da ya tabamin zuciya,
Nayi mafarki jiya daddare yadda aka nunamin a mafarkin shine Aljannah Allahu Akbar 😭
Amma Kuma an nunamin wani darasi a aciki akan mata,
yadda mafarkin ya kasance, Alllah yakaini zuwa aljannah duk Wasu kayan Alatu da ake kwatanta aljannah Allah ya nunamin Sannan Kuma Allah yayi sama Dani acikin aljannah a chan saman akwai wata hanya wacce ta rabu gida uku wata tayi gabas wata tayi yammah wata Kuma ta mike zuwa wata Kofa Mai launin Gold 🪙 a daidai wannan kofar a nunamin cewa da yawan mata basa iya wuce wannan kofar suna zuwa saidai suyi hanyar da ta tafi zuwa yammah basa iya mikewa zuwa wannan kofar,
Allah ya nunamin yadda dabobbi suke wucewa batare da wani Abu ya taresu nikuma Allah sai yabarni a bakin wannan kofar duk Wanda Yazo wucewa sai ya gaisar Dani musamman Abinda Allah yafi nunamin shine Giwa🐘 idan tazo wucewa zata gaisar Dani saina bata waje ta wuce,
bayan na farka daga wannan mafarkin na ringa tambayar kaina cewa shin Mai yasa da yawan mata basa iya wuce wannan kofar ?
Allah yasa mudace 🤲