30/11/2023
*_⬛️HASSADA⬛️_*
Darasi na ❶
*◼️Hassada shi ne: ka yi gurin gushewar wata ni'ima dake wajen ɗan uwanka, ba tare da ta dawo gareshi ba.*
◻️Allah maɗaukaki ya ce
*﴿نَحْنُ قَسَمْنَا بَيْنَهُم مَّعِيشَتَهُمْ فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا ۚ وَرَفَعْنَا بَعْضَهُمْ فَوْقَ بَعْضٍ دَرَجَاتٍ لِّیَتَّخِذَ بَعۡضُهُم بَعۡضࣰا سُخۡرِیࣰّاۗ وَرَحۡمَتُ رَبِّكَ خَیۡرࣱ مِّمَّا یَجۡمَعُونَ}*
*"Mu ne muke raba musu abinchinsu arayuwar duniya, kuma muka ɗaukaka sashinsu akan sashi da darajoji, don sashinsu ya riƙi sashi amatsayin 'yan ƙwadago. Rahamar Ubangijinka ita tafi alkhairi daga abin da suke tattarawa".*
الزخرف 32
*💡Wani daga cikin magabata yana cewa "Na lura da Hassada, sai na gane cewa lallai dukkan rabo daga Allah yake, don haka ba zan yiwa kowa Hassada ba har abada".*
◻️Allah maɗaukaki ya ce
*(وَلاَ تَتَمَنَّوْاْ مَا فَضَّلَ اللّهُ بِهِ بَعْضَكُمْ عَلَى بَعْضٍ لِّلرِّجَالِ نَصِيبٌ مِّمَّا اكْتَسَبُواْ وَلِلنِّسَاء نَصِيبٌ مِّمَّا اكْتَسَبْنَ وَاسْأَلُواْ اللّهَ مِن فَضْلِهِ إِنَّ اللّهَ كَانَ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيمًا*
*"Kada ku riƙa gurin abin da Allah ya fifita sashinku akan sashe, maza suna da rabo daga abin s**a samu, mata ma suna da rabo daga abin da s**a samu. Ku roƙi Allah daga falalarsa. Lallai Allah yakasance mai ilimi ga dukkan komai".*
النساء: 32
◻️ Manzon Allah ﷺ ya ce
*🔺"Kada kuyi Hassada, kada kuyi kore, kada kuyi ƙiyayya kada ku ruɗi junanku....".🔺*
📜رواه مسلم ( 2559 )
◻️قال ابن بطال-رحمه الله- :
*"Aciki akwai hani game da Hassada akan ni'ima. Haƙiƙa Allah ya hana bayinsa masu Imani su riƙa yin gurin abin da ya fifita sashinsu akan sashi, sai ya umarcesu da su roƙeshi daga falalarsa".*
📜شرح صحيح البخاري 9/258
◻️قال ابن تيمية -رحمه الله- :
*Abin nufi, lallai ita Hassada wani ciwo ne daga cikin ciwukan zuciya, kuma ciwone da galibin mutane basa kuɓuta daga gareta sai 'yan kaɗan daga cikin mutane. Don haka ne ake cewa: Jiki baya kuɓuta Da Hassada, sai dai, Wawa shi yake bayyana ta, Karimi kuma shike ɓoye ta".*
📜الفتاوى 10 / 124
◻️قال ابن عثيمين -رحمه الل