Rijiyar_lemo City.

Rijiyar_lemo City. Our Proudly

Wannan matashi dan ƙasar Libiya mai suna Amer yana kan hanyarsa ta zuwa aikin Hajji, sai ya fuskanci matsala dangane da ...
23/05/2026

Wannan matashi dan ƙasar Libiya mai suna Amer yana kan hanyarsa ta zuwa aikin Hajji, sai ya fuskanci matsala dangane da sunansa yayin da ake bincike a filin jirgi. Jami’an tsaro s**a ce masa, “Za mu kokarta warware matsalar, amma sai ka jira dan lokaci.” Sauran mahajjata an kammala binciken su, s**a hau jirgi, aka rufe kofar jirgin. Bayan ɗan lokaci, an warware matsalar Amer, amma matukin jirgi ya ƙi buɗe masa kofa, jirgin ya tashi.

Jami’an tsaron s**a rarrashe shi s**a bashi haƙuri, Amma Amer ya ki barin filin jirgin, ya nace da cewa, “Na yi niyyar yin Hajji, kuma In Sha Allah zan je.”

Cikin gaggawa sai ga rahoto ya iso cewa jirgin ya samu matsala, ya dawo. Aka gyara matsalar jirgin, amma matukin ya sake kin bude kofa. Jami’in tsaro ya ce masa ya rarrashe shi yace masa “Ba a rubuta wannan tafiyar za'ayi ta da kai ba.” Sai Amer ya amsa da kwarin gwiwa, “Na yi niyyar yin Hajji, kuma In Sha Allah zan je.”

Jirgin ya sake tafiya, daga baya aka sake samun rahoto cewa ya samu wata matsala kuma ya dawo karo na biyu. A wannan lokaci ne matukin jirgin ya fahimta, ya ce, “Ba zan tashi ba idan babu Amer.” s**a ɗauke shi s**a tafi, s**a sauka lafiya.

Wannan hoto ne da matuƙa jirgin s**a ɗauka tare da Ameer.

Shafin Inside the Haramain ne ya wallafa rubutun da turanci.

✍🏻 Abdulkadir Muhammad Bello

19/05/2026

Hajiya (Saro mai waina Rijiyar lemo) ta rasu!

Daga Abubakar Sadik (Baba Habu)

Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un 😭

Allah yayiwa mahaifiyata rasuwa yau 19-05-2026 da misalin karfe 6:00am, hajiya saratu sale, saro mai waina, za'ayi jana'izar ta yau da misalin karfe 10am na safe agidanta dake Rijiyar lemo Titin Danrimi ('Yan babura) kan layin Vice, muna bukatar addu'arku Allah ubangiji ya gaparta mata dan Annabin rahma ameen 🙏🏻😭

08/05/2026

Don Allah jama'a ana cigiyar wannan bawan allah sunansa Kabeer Ridwan ɗan unguwar Rijiyar Lemo ne titin baure, ya fita daga gidansa ranar talata da safe 5 ga watan Mayu domin zuwa kasuwar Wambai.

Ƴan kasuwar sun ce ya fita daga wurin karfe 3 na Rana daga kasuwa amma daganan baa ƙarajin labarin saba, dan allah duk wanda ya sameshi ya temaka ya kira waɗannan lambobin.

08036630184
07036823635
09161665937

Daga Malam Zahraddin Sulaiman Abdullahiإنا لله وإنا إليه الراجعونAllah ya yi wa Abbanmu - Malam Sulaiman Abdullahi - ras...
04/05/2026

Daga Malam Zahraddin Sulaiman Abdullahi

إنا لله وإنا إليه الراجعون

Allah ya yi wa Abbanmu - Malam Sulaiman Abdullahi - rasuwa yanzu, a yau Litinin 4/5/2026. Za a yi jana'izarsa a masallacin Kandahar, Rijiyar Lemo, da misalin karfe 11 na wannan safiyar.

Da fatan Allah ya yi masa rahama ya sa aljanna ce makomarsa, amin!

Daga: Malam Suleiman Khairul-bariyyaKHAIRUL BARIYYA  TAYI BABBAN RASHI ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHMun wayi gari da BA...
24/04/2026

Daga: Malam Suleiman Khairul-bariyya

KHAIRUL BARIYYA TAYI BABBAN RASHI ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH

Mun wayi gari da BABBAN RASHI na jigo uba ga al,ummar wanna unguwa(Alh. Abdulhamid Umar Buruntumau) wanda shine yazo ya samu mallam BABBA MARIGAYI MALLAM MUSA HUSSAIN DA SHAWARAR LALLAI MALLAM SAI YA kafa makaranta a unguwarnan haka kuwa akayi.

Gashi yau Babu ko daya acikinsu

ALLAHUMMAGFIRLAHUM WARHAMHUM WA AFU ANHUM YA ARHAMARRAHIMN.

Da fatan dai ban da wayar da power bank aka taka!
30/03/2026

Da fatan dai ban da wayar da power bank aka taka!

25/03/2026

😭👇
"Barrister bari in fada maka wannan abun, kwanakin baya mahaifiyata ta kira ni tace in taimakawa wata dattijuwa za ayi mata aiki a Asibiti ana neman Naira dubu 80,000 nace Umma ki bata hakuri abubuwa sunyi yawa, Umma ta takura mun lallai sai in dauki nauyin aikin, nace Umma ayi hakuri ga dubu 10,000 tace a'a don Allah ka biya gaba daya."

Yace mun (har ga Allah a lokacin ina da hali amma akwai wasu dawainiyoyi akaina idan na bada dubu 80,000 ban san ya zanyi ba).

Sai Umma tace "Allah zai mayar maka". Sai jiki na yayi sanyi nace mata ranar yaushe za'a yi aikin? tace 13 ga watan Azumi (just Azumin da ya wuce last week, this 2026), ranar tazo na tura Naira dubu 80,000 duk jikina yayi sanyi, ina tunanin ya zanyi don wallahi bani da Abincin da zai kaimu Sallah, ga 'ya'yana uku babu maganar dinkin Sallah a lokacin.

Yace:
Akaramakallah ranar 20 ga watan Ramadan din nan, kwana bakwai ciff da yin aikin, sai maigidana ya kira ni yace inzo Abuja inyi masa aiki za'a sayi wani fili mallakar kamfanin sa, a ranar naje Abuja, washegari aka yi ciniki in billions, Barrister na tashi da 25m in Naira.

A hakan ma Alhaji yace idan an dawo daga hidimar Sallah zai sallame ni. Babu abinda ke yawo a zuciyar ta kamar maganar da Umma tace "Allah zai mayar maka". Yace "Nayi kuka sosai, domin ban taba mallakar miliyan 5 nawa a lokaci daya ba".

Yace yanzu haka bayan Sallah zai tafi Ka'abah yayi Umrah yayi godiya. Nace Allah yasa albarka, ya taimaka, amma zan rubuta wannan labarin domin kara karfafa mutane akan biyayya ma iyaye, yace babu matsala in dai ba za'a fadi sunana ba.

Da na buga lissafi sai naga an ninka masa 80,000 din nan sau 315 kenan.

✍️ Barr. Abdul-Hadi Isah Ibraheem

CIGIYA! CIGIYA! CIGIYA!✍️ Daga Malam Ibrahim Ali Darus-Salam Rijiyar Lemo DON ALLAH JAMA'A ANA CIGIYAR WANNAN YARINYAR, ...
12/11/2025

CIGIYA! CIGIYA! CIGIYA!

✍️ Daga Malam Ibrahim Ali Darus-Salam Rijiyar Lemo

DON ALLAH JAMA'A ANA CIGIYAR WANNAN YARINYAR, MAI SUNA NANA، TA ƁATA YAU LABARA DA MISALIN ƘARFE 10:00 NA SAFE DON ALLAH IN AN GANTA A TAIMAKA A KIRA ƊAYA DAGA CIKIN WAƊANNAN LAMBOBIN
0806 778 5786
0806 774 5248

KO A KAI TA WAJAN ALH. KABIRU TELA, INKIYA ALH. KEY. GADA KUSA DA SABUWAR INDIA

KO A KAI TA MAKARANTAR TAZYINUL KUR'AN WAJAN IBRAHIM DARUSSALAM SABON TITIN ƊANRIMI AREWA DA MASALLACIN NUPAWA.
ALLAH YA SA MU DACE.

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN.Allah Ya jikan Alh. Sani Saidu Kwalam. Ya rasu a safiyar wannan rana. Anji jana'izar ...
05/10/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN.

Allah Ya jikan Alh. Sani Saidu Kwalam. Ya rasu a safiyar wannan rana. Anji jana'izar sa bayan sallar azahar a gidan sa dake Rijiyar Lemo Sabon titin Dan Rimi Gidan Magani.

ALLAH YA SA HALIN DA MUKE CIKI A KASAR NAN YA ZAMA KAMAR NA "MATAR NAN TA LOKACIN ANNABI DÃWUD (AS)"                    ...
31/08/2025

ALLAH YA SA HALIN DA MUKE CIKI A KASAR NAN YA ZAMA KAMAR NA "MATAR NAN TA LOKACIN ANNABI DÃWUD (AS)"

حَدِّثُوا عن بَنِي إِسْرائِيلَ وَلا حَرَجَ
أخرجه أبو داود (٣٦٦٢)، وأحمد (١٠١٣٤)

Akwai wata mata a lokacin Annabi Dãwud (AS) da ta shiga gurinsa cikin fushi; ta ce da shi: "Ya Annabi Allah! Shin Ubangijinka azzalimi ne ko mai adalci ne? Sai ya ce da ita: "Ubangijina mai adalci ne. Me ya faru? Sai ta ce: "Ni bazawara ce da nake da yara marayu, kanana, ba ni da komai, kuma babu wanda yake taimaka min. Ina rufawa kaina da iyalina asiri ne ta hanyar sanã'ar sãka da nake yi. Yau na yi sãka ta kalar ja, na tafi kasuwa zan siyar, kawai sai wani Hankaka ya zo ya dauke min sãkar, ya tafi da ita. kuma ita ce jãri na baki daya. Yanzu ya zan yi. Adalcin ke nan?

Sai Annabi Dãwud (AS) ya ce da ita: "Allah yana da hikima; kuma duk abin da kika ga ya yi, to akwai hikima da adalci a ciki... Amma nawa ne kudin sãkar taki baki daya? Sai ta ce Dinare daya,..

Suna cikin tattaunawa, sai ga wasu mutane su 10 sun shigo gurin Annabi Dãwud (AS) s**a ce: "Ya Annabin Allah! Yau mun ga abin mamaki. Muna cikin jirgin ruwa; a tsakiyar kogi, sai jirgin namu ya būle,.. mu dab da halaka, sai muka yi bakance 'idan Allah ya ceratar da mu, kowannen mu zai yi sadaka da Dinãre 100.' Kwasam! Sai wani Hankaka ya jefo mana wata sãka ja, sai muka toshe bular da ita,.. Allah ya kubutar da mu. Saboda haka, ga Dinãre 1000 nan ka sanya shi yadda ka ga ya dace.

Sai Annabi Dãwud (AS) ya juyo gurin wannan mata ya ce da ita: "Kin ga hikimar Allah da adalcinsa ko? Dauke wannan Dinãre 1000 [ninkin kudin sakarta sau 100] duk naki ne.

YA ALLAH KA WARWARE MANA KUNCI DA TALAUCI DA RASHIN TSARO DA MUKE FAMA DA SHI A KASAR NAN TA MU

© Mal. Aminu Bala

Address

Rijiyar_Lemo
Kano
FAGGE

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rijiyar_lemo City. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share