18/05/2026
EFCC TA MIKA WA GWAMNATIN JIHAR KATSINA KUDADEN DA TA KWATO DA S**A HAURA NAIRA MILIYAN 837
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa wato EFCC, reshen shiyyar Kano, ta miƙa wa Gwamnatin Jihar Katsina kuɗaɗen da ta kwato da s**a kai jimillar Naira 837,485,389.00 a ranar Litinin, 18 ga Mayu, 2026.
Miƙa kuɗaɗen ya biyo bayan bincike daban-daban da hukumar ta gudanar kan manyan badakalar satar kuɗaɗen gwamnati mallakin Jihar Katsina.
A shari’ar farko, EFCC ta kwato Naira 547,015,389.00 bayan gwamnatin jihar ta kai ƙorafi kan yadda aka karkatar da kusan Naira biliyan 1.3 na kuɗaɗen haraji da ya kamata a tura wa gwamnati.
Binciken ya gano cewa wasu ma’aikatan Hukumar Tara Haraji ta Jihar Katsina (BOIRS) guda shida tare da ma’aikatan banki uku sun haɗa baki wajen karkatar da kuɗaɗen da s**a fito daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa kamar World Health Organization, Médecins Sans Frontières da ALIMA zuwa wani asusun banki na kashin kansu.
Bayan gudanar da bincike, an gurfanar da mutane 12 a gaban kotu. Cikin su, mutum shida sun amsa laifi kuma an yanke musu hukunci, yayin da sauran shida ke ci gaba da fuskantar shari’a a Babbar Kotun Jihar Katsina.
A shari’a ta biyu kuwa, EFCC ta sake kwato Naira 290,470,000.00 bayan wani rahoton sirri da aka samu a shekarar 2021 ya bankado wata badakala a ofishin Akanta Janar na Jihar Katsina.
Binciken ya nuna cewa tsohon Mataimakin Ma’aji na Jiha, Sani Lawal BK, tare da tsohon Mataimakin Ma’aji Sa’adu Maiwada sun haɗa baki wajen karkatar da kuɗaɗen zuwa kamfanoninsu ta hanyar cire kuɗaɗe masu yawa daga Asusun Kashe Kuɗi na Ma’ajiyar Jihar Katsina ba tare da izini ba.
Haka kuma binciken ya tabbatar da cewa babu wata hidima da aka yi ko kwangilar da aka bayar da za ta halatta cire waɗannan kuɗaɗe.
An gurfanar da waɗanda ake zargi tun ranar 11 ga Yuli, 2023 bisa tuhume-tuhumen halasta kuɗaɗen haram da kuma almundahanar kuɗaɗe a kotunan tarayya da na jiha, inda ake ci gaba da sauraron shari’ar tare da gabatar da shaidu.
An gudanar da bikin miƙa kuɗaɗen a ofishin EFCC na shiyyar Kano, inda Daraktan shiyyar, ACE1 Friday S. Ebelo, ya miƙa kuɗaɗen ga Dakta Kabir Abdullahi Yantumaki, Babban Daraktan Tsare-tsare da Bibiya na Hukumar Tara Haraji ta Jihar Katsina.
Da yake jawabi yayin taron, Ebelo ya jaddada aniyar EFCC na kare dukiyar al’umma tare da tabbatar da hukunta duk wanda aka bai wa amanar kula da kuɗin jama’a amma ya ci amanar.
Ya ce nasarar kwato kuɗaɗen ta samu ne sakamakon ƙwazon jami’an hukumar, sannan ya buƙaci gwamnatin jihar da ta yi amfani da kuɗaɗen wajen ci gaban al’ummar Jihar Katsina.
“Waɗannan kuɗaɗe mallakin al’ummar Jihar Katsina ne, kuma muna fatan za a yi amfani da su wajen inganta rayuwar jama’a,” in ji shi.
A nasa jawabin, Dakta Yantumaki ya gode wa EFCC bisa ƙwazo da nuna ƙwarewa wajen gudanar da binciken, tare da tabbatar da cewa za a tura kuɗaɗen zuwa asusun gwamnatin jihar domin amfanin al’umma baki ɗaya.