16/09/2022
Idan munyi maganar ana zaluntar mutanen karkara, sai wasu dolaye daga cikin "yan kanzagin Gomnati dake birni sunajin haushinmu.
✓ To wannan da kuke kallo, wata baiwar Allah ce, wadda akayi gwagwarmayar kafa wannan Gomnatin ta APC da ita alokacin za6enda ya gabata.
✓Amma kash" abin takaicinma shine, bataci irin romon Democradyyar da aka yaudareta dashi alokacinda ake neman kuri'unsu ba.
✓Gatanan ana turata a Kuskus, alokacinda take naqudar haihuwa, saboda qauyen da take, wato Tinda babu asibiti, sannan babu hanyar mota, wadda zaisa asami zuwa garin Malleri dake Kwami LGA, ko Cottage hospital dake garin Mallam sidi ba.
✓ Lallai garin Tinda, garine da yake Kwami LGA, sannan garin yanada manyan garuruwa zagaye dashi, ta gefen arewa dashi, akwai Allugel da Shanin Fulani, Shanin Tera, da sauransu, sannan gefen kudu akwai garin Fegi da Maqera, da Dabar Labbo, agefen yamma akwai garin hakiminsu wato Malleri.
✓Bayan dimbin al'ummar dake wannan yanki, Allah ya h**e musu arziqin noman damuna dana rani, sannan akwai dinbin arzikin dabbobi, ganan ruwa kuma da ake kamun kifi.
✓Amma duk da wadannan arziki, da Allah ya h**e musu, basa samun romon Democradyya da ake magana, saboda duk wani abin more rayuwa sai dai wanda su s**a yiwa kansu, babu wani abinda Gomnati tayi musu na azo agani.
✓Sai ganan wannan Gomnatin yaudarar, tazo tana inganta cikin birnin jiha, ba tareda la'akari da mummunan hali da al'ummarta na karkara suke ciki ba.
✓Kuma kullum cikin qarairayin ayyuka wa mutanen karkara suke, amma basu ta6ukawa mutanen karkara komai.
✓Ya Allah kaga irin halinda s**a bar talakawanka aciki, ka hanzarta kawo mana dauki daga hannun mayaudara, ka sauya mana da wadanda s**a san dajarar talakawanka dake karkara.