Demokradiya A Yau

Demokradiya A Yau This page was design to promote, The Program DEMOKRADIYA A YAU
(1)

Jigo a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a Jihar Adamawa, Malam Muhammed Usman Shuwa, ya karɓi fom ɗin tsayawa...
13/05/2026

Jigo a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a Jihar Adamawa, Malam Muhammed Usman Shuwa, ya karɓi fom ɗin tsayawa takarar gwamna domin neman jagorantar jihar a zaɓen shekarar 2027.

Sanarwar hakan ta fito ne daga Engr. Dan Talaka (MNSE), wanda ya bayyana cewa karɓar fom ɗin alama ce ta fara sabuwar tafiya ta fata da sauyi, wadda za ta mayar da hankali kan shugabanci nagari, adalci da kuma gwamnatin da za ta tsaya kan muradun al’umma.

A cewarsa, wannan yunƙuri na Malam Muhammed Usman Shuwa na nuni da burin jama’a na ganin ci gaba, haɗin kai, bunƙasa tattalin arziki da kuma gwamnati mai sauraron koken al’umma.

Masu goyon bayansa sun bayyana cewa wannan mataki ya nuna fara gagarumar tafiya, tare da bayyana fatan samun nasara da yardar Allah da kuma goyon bayan jama’ar Adamawa.

Ana dai ci gaba da ganin karuwar masu sha’awar neman kujerar gwamnan Adamawa a jam’iyyu daban-daban yayin da ake tunkarar babban zaɓen 2027.

Jigo a jam’iyyar PDP a Jihar Adamawa, Chief Maurice Vunobolki PhD, FCA, ya mika fom dinsa na neman tsayawa takarar gwamn...
13/05/2026

Jigo a jam’iyyar PDP a Jihar Adamawa, Chief Maurice Vunobolki PhD, FCA, ya mika fom dinsa na neman tsayawa takarar gwamna a hedikwatar jam’iyyar PDP da ke Wadata Plaza a Abuja.

Masu goyon bayansa sun bayyana cewa mika fom din na daga cikin matakan tabbatar da aniyarsa ta shiga takarar gwamnan jihar Adamawa a zaben shekarar 2027.

A yayin mika fom din, magoya bayansa sun rika bayyana goyon baya tare da jaddada cewa “maganar gwamnan Adamawa ba fashi,” suna masu cewa Chief Maurice Vunobolki shi ne zabin da jam’iyyar PDP da jihar ke bukata domin ci gaba da samar da cigaba.

Ana dai ci gaba da ganin karuwar masu sha’awar neman takarar gwamna a jam’iyyun siyasa daban-daban yayin da ake tunkarar babban zaben 2027.

13/05/2026

Yadda aka gudanar da taron siyasa na AB Haske a kananan hukumomin Toungo, Jada, Ganye da Mayo Belwa, inda aka ce taron ya samu halartar jama’a masu yawa fiye da yadda aka taba gani a yankin

12/05/2026

🔥 DA DUMI-DUMI 🔥

Kungiyar Tsoffin ’Yan CPC Ta Bayyana Goyon Baya Ga Atiku A ADC..

Hon. Aminu Musa Karofi ya sayi fom ɗin tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Dutsinma da Kur...
12/05/2026

Hon. Aminu Musa Karofi ya sayi fom ɗin tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Dutsinma da Kurfi a Jihar Katsina, ƙarƙashin tutar jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Rahotanni sun nuna cewa Hon. Karofi ya kammala sayen fom ɗin ne domin nuna aniyarsa ta shiga fafatawar siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027, inda yake fatan samun damar wakiltar al’ummar mazabarsa a majalisar tarayya.

Magoya bayansa sun bayyana cewa wannan mataki alama ce ta shirin kawo sauyi da cigaba a yankunan Dutsinma da Kurfi, musamman a bangaren ilimi, kiwon lafiya, aikin yi da bunƙasa tattalin arziki.

Wasu daga cikin magoya bayan jam’iyyar ADC a yankin sun ce sun yi maraba da matakin, tare da bayyana cewa suna ganin Karofi na daga cikin ’yan siyasar da ke da kusanci da jama’a da kuma kishin ci gaban al’umma.

Sai dai ana sa ran fafatawa mai zafi a yankin, duba da yadda manyan jam’iyyu ke kara shirin fitar da ’yan takararsu domin neman kujerar.

12/05/2026

Yadda Dan takarar Kansila na ADC ya ƙaddamar da kamfe a Yoffo Ward, Mayo-Belwa a jahar Adamawa.

Hukumar Rage Talauci da Samar da Arziki ta Jihar Adamawa (PAWECA) ta amince da kulla haɗin gwiwa da Cibiyar Binciken Mas...
12/05/2026

Hukumar Rage Talauci da Samar da Arziki ta Jihar Adamawa (PAWECA) ta amince da kulla haɗin gwiwa da Cibiyar Binciken Masana’antu ta Tarayya da ke Oshodi (FIIRO), domin faɗaɗa shirye-shiryen horaswa da tallafa wa al’umma a fannoni daban-daban na sana’o’i.

An cimma wannan matsaya ne a ranar Talata, yayin wata ziyarar girmamawa da jami’an FIIRO s**a kai wa Darakta Janar na PAWECA, Dakta Michael Zira, a birnin Yola.

Dakta Zira ya ce haɗin gwiwar zai bai wa ɓangarorin biyu damar haɗa ƙarfi da ƙarfe domin ƙarfafa hanyoyin dogaro da kai da bunƙasa sana’o’i a jihar.

Ya bayyana cewa PAWECA ta riga ta horas da dubban matasa da masu digiri a sana’o’i daban-daban, tare da raba tallafin Naira 50,000 ga sama da mutane 200,000 a ƙarƙashin shirin Fintiri Business Wallet, domin tallafa wa ƙananan sana’o’i da kasuwanci.

Dakta Zira ya ce ziyarar ta zo a daidai lokacin da hukumar ke shirin fara wani sabon shiri mai suna “From Retirement to Wealth” (Daga Ritaya zuwa Arziki), wanda Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya amince da shi kwanan nan.

Ya ce shirin, wanda shi Darakta Janar ɗin ya assasa, an tsara shi ne domin taimaka wa ma’aikatan gwamnati da ke gab da ritaya su samu hanyoyin dogaro da kai da samar da sana’o’in da za su ci gaba da yi bayan sun bar aiki.

Zira ya bukaci FIIRO da ta fara matakan ƙulla yarjejeniya a hukumance domin a samu sakamako mai amfani ga al’umma.

A nasa jawabin, Kodinetan Yankin FIIRO, Dakta Ajani Sakirdeen, ya ce cibiyar ta zaɓi PAWECA a matsayin babbar abokiyar hulɗa saboda muhimmancin rawar da take takawa wajen rage talauci da samar da aikin yi.

Ya ce FIIRO na gudanar da bincike kan albarkatun ƙasa, tare da samar da fasahohi da na’urori da ke taimakawa sarrafa abinci da kayayyakin noma, da kuma ƙirƙirar hanyoyin samar da masana’antu a matakin gwaji.

Sakirdeen ya ƙara da cewa cibiyar na kuma tallafa wa masana’antun cikin gida wajen amfani da sabbin fasahohi, tare da bayar da shawarwari da nazarin yiwuwar aiwatar da ayyukan kasuwanci.

Ya yaba wa Dakta Zira bisa jajircewarsa a aikin gwamnati da kuma yadda ya karɓi tawagar cikin mutunci.

12/05/2026

*💥BOOM🔥*

Hon. Samuel Joseph (Sam Daga Damare), Ya Yaba da Dacewar Hon. Juda Amisa, inda ya ce yana daga cikin mutanen da s**a fi dacewa da kujerar dan majalisar dokokin jihar Adamawa.

11/05/2026

Yadda Tsohon Gwamnan Jihar Adamawa, Umar Jibrilla Bindow, ya karɓi fom ɗin tsayawa takarar gwamna a jam’iyyar (ADC) daga wata haɗakar kungiyoyin matasa da mata a jihar, gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

10/05/2026

A yau Lahadi, 10 ga watan Mayu, 2026, Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum ya jagoranci bikin buɗe Makarantar Marayu ta Darul Aytam, wacce ke ƙarƙashin kulawar Guruntum Orphans Support Foundation.

10/05/2026

Kungiyar masoya Hon. Aminu Musa Karofi da ake kira Aminu Musa Karofi Loyalist Forum ta gudanar da wani taron bada tallafi tare da horas da mata kananan sana’o’i a Karamar Hukumar Dutsinma da ke Jihar Katsina.

Address

Yola
652105

Telephone

+2348021453694

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Demokradiya A Yau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share