HAUSA NOVEL ONLY

HAUSA NOVEL ONLY Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from HAUSA NOVEL ONLY, Marketing Agency, Kaduna, Zaria.

12/06/2026

đź’«AUREN HADIđź’«

✍️M SHAKUR

EPISODE 🔟

*

*Ask for Hamy. Taste the difference!*
Around 5 Abba da kansa yamusu knocking kofan dakin, ita tafara tashi daga kan gadon saita dauki waynta ta kunna flash tana haskawa dan bataso ta kunna musu haske wutan dakin, tabude jakanta tadauki brush tawuce bayinsu tai brush ta dauro alwala tafito tasaka hijab tahaukan daduma tai salla ta idar, azkar tayi saita dauki wayanta takara dailing number Ummy amman wayan baya shigane at all k**an tai deactivating line nata ko wayan na flight mode bayan hannunta takai ta share hawayen das**a zubomata saita tashi takoma gado ta kwanta tai lakur.

Around 6 na safe wayanta yafara ringing, idan da sabo tariga da tasaba da wanda ke kiranta in the morning, yawanci Husna ce ke kira, especially idan akwai wani important abu ko assignment takan tambayeta kotayi, yanda take k**an bazata dauki wayan ba tamika hannu ahankali tadauki wayan takai kunne batai magana ba, Husna tace “Ahlan we need to be in school at 8 cus yau zamu fara clinic, idan muka wuce 8 bus zai tafi ya barmu saidai mu mudauki mota kanmu” shiru tayi takasa magana gabaki daya karatun ma da school din duk ji tayi yafitan mata aria, morethan awa nawa bataji daga wajen Ummy ba, ahankali Husna tace “Ahlan” murya chan kasa tace “uhnn”dan she is not even comfortable adakin, gently tace “naji zan shirya” tacire wayan daga kunnenta ta katse wayan, ijiye wayan tayi tai mirgina agadon tayi tai lamo da ace jiya da safe wara haka za’a gayamata cewa today she will not be happy or she will lost her happiness she wouldn't have believe it, Abba yasaki Ummy now she have no idea where Ummy is. Takai kusan 5min sannan ta yunkura tashi tayi ahankali saita wuce wajen kayanta tabude akwatin tadauki towel da abubuwan wanka tawuce bayin tabude ahankali ta shiga, wanka tafara kusan 10min dafarawa, aka shiga knocking kofan bayin, muryan Ramla taji tace “dalla malama kifito daga bayin mutane kafin ranki yabaci” wlh jikin Ahlan har rawa yake sabida tsabaragen tsoro kawai wani tsoron kowa take agidan tunda Ummy ta batanan, dagudu tasa ruwa tadauraye kumfan jikinta taja towel nata fari tataho tabude kofan ahankali tama kasa hada idanu da Ramla, binta dawani kalan kallon tsana Ramla tayi wani abu na kishi na tsayamata a wuya ganin yanda ruwa kebin gefen fuskanta, gashinta ya kwanta yayi nasha nasha k**an an zuba oil yana kyalli yayi wani kalan kyau bana wasaba, gashi Allah yamata shape batada jiki but then she’s b***y, akwai b***s, ga ass dinta nada shape sosai, curvy mai hips, kaganta k**an ita tai kanta sabida kyau, eye lid nata sunyi ja sun kumbara sabida kuka, yanda Ramla kejin kishi kasa magana tayi, wani kalan bangajeta tayi tashiga ciki Ahlan tai k**an zata fadi tai maza tadafe bango tana sauke ijiyan zuciya da sauri da sauri sai tawuce ahankali tazo wajen box dinta, Maryam da idanunta suke abude tabita da kallo bata cemata komiba.

Goge jikinta tayi saita dauki cream tashafa, saita ciro bra da pant dawani simple gown na atampa fitted mai pattern brown da n**e taciro n**e gyale, bata saba shiryawa gaban mutane ba, dan d**o kanta tayi ahankali tadan waigo hada idanu tayi da Maryam dake kallonta saita maida idanunta kasa dasauri irin na yanayi na kunya, Maryam taja gajeren tsaki cikin cranky voice na bacci tace “ki tsiya anan don’t get ready” takai kusan 2min ahaka saita mike tsaye tabama Maryam baya tashiga shiryawa Maryam itama tadauke kai abinta ganin she’s really not comfortable, tsaf ta shirya babu komi a fuskanta banda mai data shafa, saita wuce gaban madubi tasaka nosemask sannan tai rolling gyalen kanta ya zauna dass k**an balarabiya, body spray nata da turare ta feffesa that smells so good sannan tadauki wani karamin handbag tasa notebook guda daya sabida jotting sannan tahada jakanta ta maida back tadauki wayanta har lokacin Ramla na bayi ahankali tace “Ya Maryam natafi” Maryam tadan kalleta the thing is she doesn’t like the girl with all the story da Mom tafada musu on abinda Maman Ahlan tama Mom but then batasan mesa ba deep down tausayinta takeji, she can’t be wicked to her, cikin dan fushi tace “nace kifadamin ne”? Girgizamata kai Ahlan tayi tawuce wajen kofa tasa hannu zata bude kofan k**an daga sama Maryam tace “saikin dawo” dan juyo da kanta Ahlan tayi ta kalleta amman hartaja bargo tarufe kanta saita bude kofa ahankali tafita daga dakin tajawo kofan.

Babu kowa a falon sama but daganan tanajin kamshin turaren Abba, tahowa staircase tayi Abba na zaune shi kadai a falo yasha manyan kaya dake kyalli yana sipping shayi yana duba jarida a hannunsa, Abba nafita da wuri, baya kawo jama’ansa gida, kowa waits for him ko a office ko a party house nasa na siyasa, sauke jaridan yayi yatsare ta da idanu dudda akwai nose mask kan fuskanta, tundaga gown na jikinta yake kallo zuwa rolling din da jakan data dauka da clean labcoat dake hannunta saiya kallo agogon hannunsa is just 7:30 now, hakanan idan taga Abba gabanta har faduwa yake bawai dan yataba mata fada ko wani abu bane no, hasalima tunda dai tai girma tai wayau bazata iya cewa ga rannan da Abba yataba mata fada koya doketa ba but not just her dukansu Allah ya daura musu shakkan mahaifinsu, baya fadi aketare kap gidan nan.
Har gabansa tazo saita duka ahankali kanta akasa tace “ina kwana Abba” wannan karan ijiye jaridan yayi gabaki daya a gefensa yace “sauke nose mask din” hannu tasaka ahankali tasauke kasa still kanta akasa, anatse yace “kin tashi lafiya” ahankali tace “eh lafiya lau” anatse yace “why are you going to school early today?” Ahankali tace “zamu fara clinic yau, daga school by 8 bus zai kaimu general hospital” anatse Abba ya jinjina kai yace “okay jeki sa wani abu a cikinki zan saukeki” gyadamai kai tayi tamike zata juya yabata hannunsa yace “give me ur bag and the labcoat” dasauri tazare jakan daga shoulder tabasa da labcoat yana cikin karba daidai Hajiya tafito daga kitchen tareda yar aikinta dake sanye da uniform tana rike da tray, wani abu taji ganinsu ahaka tadaure takarasa tahowa itakuma Ahlan tajuya zata dinning Abba yace “zo zauna kici wannan” dasauri Hajiya tace “ranka shi dade ga abinci dayawa saitaci naka” ko tanka Hajiya baiyiba yace “zauna Ahlan” ahankali tace “ina kwana Hajiya” tana kokarin zama Hajiya kawai tajuya tace “lafiya” mai aikin tabita abaya Abba yakalli Ahlan dake kallon abincin yace “eat” kallon abincin tayi akwai kunu atare, kosai, sai chips da eggs da gasashen kaza, ahankali tace “Abba bazan iya cinyewa ba” calmly yace “nasani” kunun tadauka da spoon tafaraci da kosai guda daya saita dauki chips da egg din tafara ci ta ijiye kunu Abba kawai kallonta yake, chips da eggs kawai taci sosai sai tasha fresh juice na watermelon da akayi ta tsaya Abba yace “kin gama” gyadamai kai tayi yace “okay tashi mutafi” mikewa tayi zata dauki tray na abincin yace “leave it there muje” wucewa yayi tabisa har waje inda driver da security ke binsa bayan jeep din aka bude musu Abba yakalleta yace “shiga” ita tafara shiga sai shi yashigo aka rufe musu kofan aka jasu wayan Abba na ringing daga wayan yayi yakara a kunne yay shiru chan yace “I will be at the office in the next one hour zan sauke Ahlan a makaranta ne Excellency” yadanyi shiru yace “Nile university department din medicine” anatse Abba yace “okay then let’s meet there” Abba ya katse wayan tareda sauke ijiyan zuciya yadan kalleta window take kallo tana kallon hanya, k**an daga sama yace “kinada wata matsala da zama tareda su Hajiya”? Dasauri ta juyo da kanta saita girgiza kai tace “a’a” bai kara cewa komiba yabude wani file dake dauke da tambarin ACP yace “zamu fito takara under jam’iyyan ACP amatsayina na mataimakin shugaban kasa, Alhaji Hassan kuma shugaban kasa” tunda ta taso Abba has been a politician he held different offices he’s so ambitious, ita batada any interest na politics ita bamatason mutane susan waye Babanta, bamatason asan fuskanta, ita bata ma alfahari da irin abubuwan nan, su Ramla ne dai keson irin abubuwan, sunason asan Babansu wane ne.

Alhankali tace “Allah yabada sa’a Allah ya taimaka” murmushi yayi irin na manya kadan yace “Ameen” ahaka s**akai university dinsu already parking space din gawata arniyan jeep da kuma motan yan sanda wajen suna karasa parking aka bude bayan motan wani attajiri yafito yana gyara Babban rigansa ga glass a idanunsa shima Abba na fitowa daga motan mutumin yace “why kake yawo da just one security one driver kana presidential aspirant Alhaji”? Yayi maganan yana mika masa hannu s**a kashe while Ahlan na saukowa daga motan ahankali tana kara gyara nose mask dinta tadan duka tace “ina kwana” Alhaji Rabe yabita da kallo yace “wai Ahlan ce tai girma har ake karatun medicine, Ahlan dana radama suna? Rabon danaga Ahlan namanta su Rahma da Maryam nasani kasan suna zuwa gida”? Abba yayi dan murmushi yace “itace, wannan itace likitan gidan karatu yasa bata yawo” Alhaji Rabe ya gyadakai yace “ba shakka, tashi tashi daughter” yakalli Abba yace “but mesa kabarta take medicine a Nigeria”? Abba yace “is a rule in my house all yarana mata bana turasu kasan waje karatu, they grow and study agabana” Alhaji Rabe yace “Masha Allah hakan nada kyau kuma, wani year k**e yanzu daughter?” Ahankali Ahlan tace “4th” Alhai Rabe yace “Wai Wai Wai tayi sauri I think she’s 20yrs yanzu ko”? Abba ya gyadamasa kai feeling very proud dinnan yace “eh, at 17 tafara” Alhai yace “ba shakka” ahankali Ahlan tace “Abba natafi” kafin Abba ya amsa Alhaji Rabe yace “tsaya tsaya” yataba aljihun sa ya ciro bandir na yan 100dollars yace “ga wannan kiyi break” girgizamai kai tayi tana komawa baya dasauri tadan duka tace “a’a nagode Allah ya amfana” wani dariya Alhaji Rabe yayi yace “wow Excellency Muhammadu kaba yaranka tarbiya kap dinsu Masha Allah now I even feel more confident to go on this big journey with you, gashi tunda bazata amsaba kai amsan mata” murmushi Abba yayi feeling very proud da yabonsa da Alhaji Rabe yayi yakalli Ahlan dake gefensa yace “amsa kitafi” gyadamai kai tayi saita dawo taduka tareda sa hannu ta karba tace “nagode Abba Allah saka da alkhairi” Alhaji yace “maza tafi Allah yayi albarka, Allah baku sa’a nifa zan cigaba da cin sugar we have a doctor in the family” dashi da Abba s**ai dariya while Ahlan tawuce da sauri dan 8 tamayi ga katuwar doguwan bus dinsu gaban department nasu duk s**a bita da kallo, tashiga bus din anatse, Alhaji Rabe yakara kallonsa yace “Goodjob training girl child, I think Ahlan ce zabina ba Rahama ba” murmushi Abba yayi yadanyi jimmm Alhaji Rabe yakafesa da ido yace “wani yafito ne”? Abba yace “ko daya Excellency” Alhaji yace “ita nazabawa Alameen” Abba ya jinjina masa kai yace “press is ready”? Alhaji Excellency yace “yes da duka party members dinsu, let’s go mubasu this new na HADA AUREN YARAN MU dazamuyi!” S**a kwashe da dariya irin na manyan s**ai musabaha s**a shiga mota s**a wuce.
Meson group a WhatsApp
0816 667 4823

12/06/2026

*FITAR RABO*🌹
{ Love story }

NA
*AUTAR MANYA*

009

Wani irin wahalallan yawu ta haɗiye lokacin datai idanu huɗu da innah da ya salisu da ya jidu da maryam suna nufo su sedai basu riga da sun ƙaraso wajan nasu ba.
Cikin tashin hankali take bin fuskarshi da kallo wadda ta cika da zallar mugunta babu alamun sassauci atare da shi.
"Dan Allah ka rufamin asiri idan yayina da mahaifiyata s**a ƙaraso s**a ga hannayen mu sarƙe dana juna tabbas na kaɗe har ganyena kayi haƙuri dan Allah"
Tafaɗa tana fincikar hannunta daga riƙon dayayi mata sedai k**ar tana jan dutse ne sema wata irin matsa daya ke yiwa tsintsiyar hannun nata.
Gumin azaba na tsatstsafo mata wani fitsari na kuma taho mata haɗe ƙafafu take jikinta na tsananin rawa tabbas yau se su ya jidu sunyi watandar ta agida muddin s**a zo s**a tarar da ita a yadda suke a yanzun.

Seda yaga dama dan kanshi ya sakar mata hannun adai dai sanda ya sakar mata hannun kuma su Innah s**a ƙaraso wajan sedai Anyi rashin sa'a yana ƙoƙarin juyawa yayi tafiyarshi s**a haɗa idanu da ya Jidu wanda yayi saurin jada baya yana mai ƙarewa ZAKI kallo wanda ya juya yayi tafiyarshi bai kuma bi takan Nuriyyah ba.

Gaba É—aya wani irin kallo su Innah suke aika mata mai tattare da zargi yau bata ganin soyayya da tattali a idanun innarta se tsabar kallon tuhuma da zargi.
Duk da tana da tabbacin su innah basu ga sanda ya sakar mata hannu ba amman tana da tabbacin sunga tsaiwarsu tare.
Muryar ya jidu daya ɗan matso gaba bayan yaga ƙulewar Zaki ita ta dawo da ita daga duniyar tunanin data faɗa.

"Uban me k**e yi anan keda wancan É—an iskan É—an daban dama gidansu kika cewa innah zaki? kenan kin sanshi kuna mu'amala domin a tarihin rayuwar zaki babu wata macen daze irin wannan tsaiwar da ita koda kuwa Ć´an uwan sa ne"

Maƙogwaron Nuriyyah ne ya bushe wata ishirwa tana sasaƙarta jikinta ya tsananta rawa hawaye s**a wanke kumatunta jin wannan dogon ƙazafi Daya jidu ke lafto mata.

Tsawar ya salisu ita ta kuma firgitata.
"Wuce mu tafi gida Ć´ar iska dama wajanshi kika ja maryam kuka tafi har k**e wayancewa da allura to Allah ya tona miki asiri"
Innah bata iya cewa komai ba haka maryam sedai binta da idanu da sukeyi.
Bata da bakin magana domin yawun ya bushe haka tabi bayansu Suna tafe tana tunanin wai iya ganin su da akai tare yaja mata matsala ina ga kuma lokacin daya riƙe mata hannu lallai inda idanunsu yakai da ta kaɗe har ganyanta.

Suna shiga soro taji an shaƙota ta baya an tankaɗa ta ba kowa bane se innah wadda ta wurga Nuruyyah tsakar gida ta janyo itace ta hau bugunta ba ji ba gani.

Baba sabuwa ta fito tana janye innah amman innah taƙi janyuwa sema ƙara bugun Nuri data ke maryam ta gigice itama ta saka kuka tana cewa.

"Wallahi innah kawai hasashen ya jidu ne amman dagani har nuri bamu san shiba kuma na gaya miki dama taje tai musu magana akan sun hasketa da tourch light shine ɗayan ya zaro wuƙa yayo kanta shine wannan ɗan daban dana ji ya jidu yace sunanshi Zaki ya mari wanda ya zaro wuƙar daga nan muka gudu nida wanda muka tsayar muna tambaya nazo gida a hanya na tari su ya jidu na gaya musu shine kema nazo na gaya miki mun fita muka haɗu dasu ya jidu muka ƙarasa muka gansu a bakin layi innah kika sani ko rakota yayi hanya kya bari ai kiji me zata ce"

Maryam ta ƙare maganar tana gunjin kuka tana yarfe hannu k**ar ita ake duka.
Cike da faÉ—a Baba sabuwa take magana.
"Haba Binta so k**e ki kashe Nurin ne waye mai laifi inba maryam ba dan ubanta data ga za'a kashe Ć´ar uwarta mai yasa ta gudu bazata tsaya ba ku kuma shine ba bincike kuka sakot da faÉ—a kema kin biyewa su jidu yau kina dukanta"
Baba sabuwa ta faÉ—a lokacin data ke janye Nuriyya wadda tsabar kuka yasa muryarta dashewa.

Dama su ya jidu sun tsaya ƙofar gida shiyasa gidan ba kowa se innah da maryam da baba sabuwa da Nuriyyah kuma koda ma suna gidan sedai su daɗa mata wani dukan.

Adai dai sanda innah ke kokarin janyo Nuri ta kuma naÉ—a malam ya shigo tsakar gidan yana magana sama sama.
"Binta kasheta zaki ne ku wasu irin mutane ne duk abin da ake muna rumfa muna saurara bazakiji ta bakin yarinya ba seki hau naÉ—arta zonan uwata share hawayen ki"
Yafaɗa yana mai riƙo Nuri datake ta Gursheƙen kuka k**ar ranta zaya fita.
Yarda itacen Innah tayi tana mai kallon Nuriyyah da ɓacin rai.
"wallahi tallahi ni binta bazan kaffara ba idan naji wata magana a tsakaninki da wancan É—an daban sena lahanta ki sena fasa miki fatar jikinki ina zamana lafiya bazaki haÉ—amin masifa idan banda shashanci ma ina ke ina maza mai yakaiki wajansu mai yasa ya rakoki har nan nikam bamma yarda dake ba karkiga ina sakar miki wallahi bazan lamunci shashanci da sakacin banza ba"
Innah takai tana mai shigewa É—akinta tabar malam da Nuriyyah dasu baba sabuwa anan wajan.

Lallai tunda innah ta saka hannu ta daki Nuri yau kam ranta ya ɓaci kuma ba ƙaramar tsanar wannan ɗan daban tayi ba.
"wallahi malam ka tambayi maryam bamma sanshi ba kuma tsakani da Allah karnuka ya sakar min shine na sanya mai kuka ya rakoni bakin layin nan amman ni ban taɓa ganin shiba seyau amman shine innah tahau buguna"
TafaÉ—a tana cigaba da kukanta.
"To inma kin sanshi daga sama ya faÉ—o idan ya kasance É—an iska ba uwa ce ta haife shiba mu munsan yaya namu zasu kasance wannan ma ai sakarcin banza da wofi ne shi É—an daban ba mutum bane ba"
Cewar baba sabuwa tana mita.
Fitowa innah ta kuma yi a zuciye tana mayarwa da baba sabuwa martanin cewar.
"Ki bashi maryam mana, Dayake ɗan iska ne za'a haɗa shi da ƴata wallahi bana ƙaunar yaron ban taɓa ganin shiba ko yau ma ban ƙare masa kallo ba amman yadda naji su Abdul-majeed na faɗin halinshi nina san ba mutumin arziƙi bane sabida haka wallahi idan na kuma ganinshi dake se ranki ya ɓaci ko allurar na soketa bazaki wa uwar tashi ba"
Innah ta faÉ—a tana mai komawa É—aki.
Salati malam yahauyi yana kallon Ikon Allah na yadda innah ta botsare cikin lokaci ƙalilan.
"Uwata jeki É—aki seda safe Allah ya rufa asiri"
Cewar Malam.
"Wallahi malam baba sabuwa ban sanshi ba maryam na sanshi?"
Nuri ta faɗa cikin tausayin kanta tare dajin wata irin ƙiyayyar zaki har cikin zuciyarta.
Murmushi malam yayi tare da ce mata.
"Na yarda uwata domin bazaki rantse a ƙarya ba jeki kwanta shi kuma Allah ya shirya shi"
Baba sabuwa da maganganun innah s**a É—an sosa mata ranta itama É—akinta ta nufi komawa malam ma na kokarin fita ya jidu ya shigo yana kallon malam yace.
"Yawwa Baba wallahi gwara da Allah yasa ka shigo baba mudai bazamu ga wannan baƙin lamari agidanmu ba shahararran ɗan daba mai tara yara ya basu kayan maye dashi Ta tsaya a waje kowa na kallonsu wallahi Zaki ba mutumin arziƙi bane baba"
Ya jidu ya faÉ—a yana makawa Nuriyyah harara!
Murmushi malam yayi domin ya fuskanci k**ar akwai dabi tsakanin nuri da jidu kasancewarsu sakwanni.kana yace wa jidun.
"Zaka iya rantsuwa akan cewar akwai alaƙa tsakanin uwata dashi yaron?"
Duru duru jidu ya hauyi don baze rantse a ƙarya ba.
Dan haka ya kasa magana seya hau sosa kan shi.
"Sabida haka ku dena ƙazafi hatta kiranshi ɗan daba da kake da ɗan shaye shaye muddin idanunka bai gani ba wallahi seka tsaya gaban Allah"
Malam ya faÉ—a yana mai ficewa daga gidan.
Cike da tsananin Tsoro Nuriyyah ta nufi ɗakin Innah ta raɓa can ƙarshen gado ta kwanta yunwar data keji ta kau a cikinta se tsananin tsoron dake cike a ranta.
Bini bini ta shafo bakinta dayay suntum ya kumbura sabida duka har tunanin fita take a goben da wannan kumburarran bakin ahaka wahalallan bacci yayi gaba da ita.

A ɓangaren Zaki kuwa..........
Meson complete WhatsApp
0816 667 4823

12/06/2026

❤‍🔥❤‍🔥 *AUREN YARJEJENIYA* ❤‍🔥❤‍🔥

*13&14*

*Bayan kwana biyu*

kwana 2 kenan da zartar da mafitar da Abdallah ya yanke musu"wanda yayi daidai da saura kwana 1 wa'adin kwanakin da baba yabama ummu su cika"to Alhmdllh ummu tun jiya ta sanarwa mama ta fidda miji"ta nuna mata dama sun jima da Abdallah suna son juna sai yanzun data masa zancen zata fidda wanda takeso yace"shine zai turo"da farko mama tace"ah ah"Amma da Aminu da ummu da s**a mata bayanin babu matsala ta Amince"saidai mama dataji wai Abdallah mohd jibo ne tayi mamaki dg ita har Aminun"sannan kuma Ajiyan taje har wajen ummar lawisa s**ayi mgn game da Abdallah da kuma Abban lawisa yabinciki halayensa kafin su sanar da baba wata fidda"to Alhmdllh yau da safe umma da mama s**ayi waya bbu wata matsala Abinciken da Abba yayi "cikin gidan kuwa goggo luba tama gama yadda ummu babu wanda zata fitar"tasha kuma Alwashin bazata tab'a bari tayi Auren hutu ba....ummu kuwa har ranta hankalinta yak'i kwanciya da wannan Auren"badan tasoba tadai Amince"tun safe takeso ta kira Abdallah tasanar masa ta Amince Amma tana jin shakku....misalin k'arfe 5:35 pm"ummu na zaune kan kujera A parlourn su tana chats"mariya ta shigo parlourn bbu ko sallama tace"Anty ummu baba yace"kizo"saida gabanta yafad'i ta kalleta tace"jeki gani nan"mama dake d'aki ta fito ta kalleta tana fad'in kije kisanar masa kin fidda"nasan dai be wuce zancen ne zai miki"in sha Allah ubangiji bazai tab'a bari mu tozartaba"ummu batayi mgn ba ta d'auki mayafin doguwar rigar dake jikinta ta yafa ta fito ta shiga d'akin baba"goggo luba dake zaune tsakar gidan ta bita da kallo harta b'acewa ganinta...da sallama ta shigo cikin d'akin ta duk'a k'asa ta gaishesa"be Amsaba sai tambayar daya jefo mata gun cewa" kin fitar ko baki fitar ba? na fitar baba Amma sai zuwa nanda kwana 3 zai turo"bbu matsala har zuwa sati ma"dan bana gaggawa sbd Aikin shed'an ne"saidai muddin sati yacika zuwa kwana 10 be turoba zakiji hukuncin dana yanke"batace komaiba tayi shiru"ki tashi ki bani waje"sosai ranta yasosu"ta rasa meta kashewa mahaifinsu Aduniya dayake nuna mata tsana da tsangwama?? ta tashi ta fito dg cikin d'akin"yanayin yadda goggo luba ta lura da fuskarta bbu walwala sai tayi zaton bata fidda mijin ba"sosai ranta yayi fari k'al"ummu kuwa can k'uryarsu ta shige k'irjinta na tsananta bugawa ta zaro card d'in Abdallah dg cikin jakarta"ta zauna gefen bed ta kwafi number d'insa"cikin fad'uwar gaba da tsoro tayi dealing d'in number d'in"busy tajita hakan yasa ta kife kanta samqn pillow tayi shiru"sai bayan mintina 5 sannan ta koma kira aikuwa ta shiga tafara ringing"sai gab da zata tsinke Aka d'auka Amma ba'a yi mgn ba"Ta girgiza kanta tana mamakin zafin kai irin na Abdallah"ko sallama Ai yayi tunda ya d'auka"sanin halinsa zai iya kashe wayar yasaka tayi saurin yin sallama cikin siririyar muryarta"dg d'ayan b'angaren big man dake zaune Akatafaren office nasa k**ar Ak'asar turai"kujera na lulawa dashi iskan fanka da sanyin AC na dukan jikinsa"yatab'e baki domin sarai yagane ummul khairy ce"be Amsa sallamarba cikin cool voice d'insa yace" wacece?"kiyi gaggawar sanar mun dan bana tsayawa jin shirme"idan kuwa bakida mgn me mahinmanci maza kashe wayar ki"dg haka yayi shiru yana jiran jin me ummu zatace??"batayi mamakin jin kalamansa ba"saita basar tace"ummulkhairy ce"dama kan maganar da muk...ke dallah banganekiba"kimun bayani ta yadda zan gane"zaki k**a yi mana surutu haka bbu kamun kai"koda yake dama ba k'auyen mutum ina yaga wani kamun kai.... uhmm! nasan kagane ka nuna baka ganeba"zancen kamun kai dakake mgn ban d'aukeka cikakken namiji ba b***e har na tsaya nayi wani kamun kai Agaban ka"Abinda nasani kawai kowa tushensa A k'auye ne....K! yafad'a Atsawace"yanzun da kika nuna mugun hali naganeki ko baki fad'a ba"fad'i Abinda yasaka kika kirani"maida mun mgn kuma ki cigaba dayi karki fasa"laifin waye idan banakaba"kaine kaja na maida maka mgn"dama na kiraka ne sbd nasanar maka na Amince"doguwar ts**a yaja yayi shiru"saida ya mula yasha Iska kafin yace"wannan tsohon zance ne da kin Amince tunda dama nasanar miki dole ki Amince"na riga na gama mgn bana buk'atar Amincewar ko"kin sanarwa yaron da kuke soyayya dashi?"yafad'a yana yatsina fuska k**ar yana ganinta"na sanar masa ya Amince"zamu had'u a gold stone dani dakai dashi muyi mgn"yaushe?"duk sadda katashi"gobe da yamma mu had'u can"saidai wlh muddin kika mun rashin kunya gabansa ko gayan maganar banza wlh tattakaki zanyi Agaban nasa....batace komaiba ta kashe wayar tana fad'in kaji dashi fitinanne.....
washe gari misalin k'arfe 5:11 pm"ummulkhairy ce zaune kan kujera"gefenta mubashshir ne"wanda yau da safe yadira Agarin sbd yana Abuja"ya shirya cikin milk d'in shadda"zuciyarsa fal kishi"yanaso yaga waye wanda zasuyi wannan Auren da ummu??"yayinda ummu ta shirya cikin k'uru Adakarta"sabon leshi ne na sallarta red colour me zanen golden tasaka"ta yafa mayafi golden Amma batayi make up ba"tun wajen 4:30 sadda s**a iso ta turama Abdallah text sun iso"Amma gashi zaman mintina 41 s**ayi wajen shiru be iso ba"tasan dama tunda yanaji da girman kai Ai bazaizo kan lokaciba"idan kuma shine Am ba daidai ba yayi wulak'anci son ransa....kinga gaskiya inada Abin yi idan bazai zoba kawai natafi"cewar mubashshir yana jan tsaki"ummu batayi mgn sbd tasan besan waye Abdallah ba"wayarta ta d'auka tafara k'ok'arin kiransa"yana ganin kiran yamata banza"dama kuma suna dg waje kusan mintina 10 kenan da isowqrsu Amma yasha Alwashin bazai shigoba sai ta gaji da jira ta kirashi"sosai ranta yab'aci da k'in d'aukar wayar da yayi.....cikin nutsuwa had'e da Aji big man yashigo wajen"cikin takunsa na zaratan mazan da s**a Amsa sunansu maza"yasha wankan manyan suit dark blue"takalmi da Agogo duk dark blue ne yasaka"yayi kyau Abin saidai ace masha Allah!yayi bala'in tsare gida"wanda hakan ba k'aramin kyau yamasa ba"body guards nasa su shidda suna biye dashi dg baya"tunda ya shigo hankalin maza da mata yakoma wajensa"duk Inda ya gifta saiya bar musu ni'imtaccen k'amshin turarensa"directly Inda ya hango ummu yanufa"tunda taji zuciyarta na tsananta harbawa ranta yabata big man ya shigo wajen"da sauri ta juyo ta hangosa yana nufo Inda suke cikin nutsuwa"cikin second 5 ta k'are masa kallo tana fad'in masha Allah! beda Aiki sai saka k'ananun kaya"ta fad'a Aranta"saidai yau taji yamata wani irin mugun kwarjini....ummu bakice komai ba ,kodai mutafi kawai?"cewar mubashshir"gaya nan fa"bece komaiba yajuya bayansa s**ayi 4 eyes da big man"k'irjinsa yabuga ya juyo ya kalleta yana fad'in banga kowaba sai Abdallah mohd jibo gasu nan zasu wuce"shine ai! kafin yayi mgn k'amshin turaren big man ya dira Awajen"da hannu yayiwa body guards nasa Alamar karsu k'araso su jirashi"befi taku ukku ba yayi ya iso gaban table d'in dasuke zaune gabanshi "cikin taushin muryanshi ya musu sallama"wanda ummu tayi bala'in mamaki"itace tayi k'ok'arin Amsa sallamar tasa"mubashshir kuwa tsabar mamaki yakasa mgn"sannan yakuma yi bala'in raina kansa dayaga Abdallah yong bolonia"Abdallah be tankawa kowa ba yaja kujera ya zauna yana danna waya"kyakykyawar fuskar nan tasa a murtuke"y'allabai sannu da isowa"cewar mubashshir cikin rawar murya"yama kasa had'a ido da shi"ummu kuwa mamakin rikicewar mubashshir dayaga Abdallah takeyi"da yauwa Abdallah ya Amsa yana shan Alwashin bazaima ummu mgn ba muddin ba itace ta fara masa ba"kusan second 30 bbu wanda yayi mgn Acikin su"kanta ayk'asa tace"ina wuni?"lafiya"dama gashi nan mun gama mgn dashi"d'ago kansa yayi yakoma kallon mubashshir"shi kansa sai yaga k**ar ummu tafi k'arfin wannan saurayi"Amma saiya tab'e baki cike da izzah yace"it's okay"dama nace tazo dakai ne"dukda banida tsarin maimaita mgn"kuma nasan ta maka bayani"so bbu damuwa zan Aureta duk lokacin dakaga katashi Aurenta kamun mgn zan sakar maka ita ka Aura"sai Abu na k'arshe shine zaka dena zuwa wajenta da kiranta yanzun sbd za'a saka mata rana"kulaka zai sakq mutane su zargi wani Abu"idan Anyi Auren zaka iya cigaba da mgn da ita banida matsala ko damuwa da hakan"sbd Aure ne bana dindin ba"kowa kuma harkan gabansa zaiyi bbu ruwan wani da wani"sai warning d'ina dakai da babbar murya banaso koda wasa kasanarwa wani ko wata Ainahin irin Auren da zamuyi da ita"idan kuwa naji maganar hmm! yafad'a yana d'allah yatsunsa biyu s**ayi k'ara"daga haka be koma mgn ba"itadai ummu shiru tayi domin duk kalamansa sun mata sai abu d'aya dayace bayan Auren su cigaba da waya da mubashshir"dukda tasan Auren da s**ayi Amma Ai duk Aure Aure ne"Allah bbu ruwansa da wasa tsab za'a rubuta mata zunubi idan takula wani...to y'allabai duk naji zan kuma kiyaye"na barka lafiya"sweet heart ina dg waje "dg haka ya mik'e tsaye "ummu kanta kawai ta gyad'a masa"yana barin wajen ta tab'e baki tana fad'in zaman me kakeyi da bazaka tafi ba?"tamkar da bango take mgn"yamata banza"ta tab'e baki tana k'ok'arin tashi taji Amon tattausan muryanshi yana fad'in gaskiya na tausaya miki"ta kallesa taga yana murmushi me wuyar fassara"Akan mefa kenan?"sbd wannan Abin da kika d'auka Amatsayin masoyi"dama shine k**eso?"kaga dan Allah kabarni da wasu k'ananun mgn"narasa meyasa idan baka k'untatamun ba bakajin dad'i?"shiru yamata yana d'aukar wayarsa da sa'ada ke kiransa"idan bbu wata mgn nizan tafi"cewar ummu batare data kallesaba"be kulataba sai mgn yaci gaba da yiwa sa'ada ba'a majin meyake fad'a"bayan yagama wayar ya mik'e tsaye beko kalletaba yyi tafiyarsa...ta tab'e baki itama tatashi ta fito ta samu mubashshir yagaji da jiranta yatafi"wanda tayi mamaki sosai.....
kwana biyu da faruwar hakan"ummu na zaune a parlourn su da yamma tana markin d'in CA text ta É—alibanta"yayinda mama ke zaune tsakar gidan tana shan Iska"goggo luba ma na zaune tayi kwad'on tuwun ruwa da daudawa tanaci tana jan yaji....wayar ummu tayi ringing"dubawa tayi taga bak'uwar number ce"d'auka tayi tana yin sallama Ahankali"dg d'ayan b'angaren k**al ya Amsa yana fad'in ranki yadad'e Anyini lafiya?"ta Amsa da Alhamdllh"masha Allah! sunana k**al! big man yabani contact naki"pls idan kina gida ki turomun Address d'in gidanku zanzo yanzun zamuyi mgn idan babu damuwa"shiru ummu tayi tana tunanin wato shiyafi k'arfin zuwa gidansu shine zai turo wani"to Inda ta godema Allah itama bata buk'atar zuwan nasa"koyace zaizo bazata bari yazoba b***e idan yaga gidansu yamata gorin cemata talaka bak'auya...kina jina ummulkhairy?"Eh inaji bara naturo maka Address d'in yanzun"dato ya Amsa"ita kuma ta yanke wayar"bayan ta gama tura masa tayi tagumi tana tunanin dame k**al zaizo?"Anya batayi kuskuren Amincewa da wannan Auren ba?"tabbas big man ba k'aramin mutum bane"karma Ayi zaton kwad'ayi dason Abin duniya yasaka zata Auresa"shin idan Anyi Auren wane irin zama zasuyi ma?"zai barta taci gaba da Aikinta?"wanda Aikin nan shine komai nata dana mahaifiyarta....tana wannan dogon tunanin taji sallamar yaro yana fad'in wai Ance ummul khairy tazo inji Abdallah! k'uri da ido goggo luba tayiwa d'an Aiken gabanta na fad'uwa"mama dake lura da ita tayi murmushi me ciwo kafin tace"jeka gata nan zuwa"dg haka mama ta mik'e tsaye ta nufi cikin d'aki"goggo luba kuwa y'arta ta kira d'aki mariya"tasanar mata idan ummu ta fita ta bita taga da waye suke mgn??....mama ta dubi ummu tana fad'in kiranki Akeyi fa nasan kuma kinji ko?"Eh yanzun zanje Ai"ki tashi ki k'ara saka turare mana"dato ta Amsa ta wuce ciki tana mamakin meyasa k**al zaice Abdallah ne?"da wannan tunanin ta d'an fesa turare ta yafo mayafi samqn red d'in Atamfar jikinta ta fito dg cikin d'akin"bbu kowa tsakar gidan"goggo luba na hangenta ta taga harta fice dg cikin gidan....
k**al na zaune samqn motarsa yana danna waya"yasha gayunsa cikin k'ananun kaya yanata k'amshi"kasancewar shima wajen gayu badaga baya ba"cikin nutsuwa ummu ta k'araso da fara'a samqn fuskarta tamasa sallama"yad'ago kansa ya Amsa yana fad'in kin zata da mutumin mukazo shine aka shanyani?"ah ah nasan kai d'aya ne"shi kuma Ai bankai matsayin dazaizo k'ofar gidan muba"ba haka bane ummulkhairy"tayi d'an murmushi ta gaishesa"Ahaka mariya ta fito dg cikin gidan tana tsaresu da ido k**ar tv"sai kuma ta koma ciki Aguje"ummu tayi murmushi Aranta"dan tasan uwarta ce ta turota "taga kuma mamaki da rud'ewa A samqn fuskar mariya"sbd ganin k**al datayi"yanzun Inda Abdallah s**a gani k'ilan sumewa mariya zatayi sbd mamaki....inaso kibani Aron hankalinki muyi mgn ta gaskiya ummulkhairy"Ahankali tace"ina sauraronka"da farko dai sunana k**al"ni Abokine wajen big man"yanzun haka insha Allah nan bada jimawa zan Auri wata cousin d'insa"yamun bayanin irin Auren da zakuyi sbd shine mafita Agareku dan gane da matsalar da keda shi kuka fuskanta ta fidda wad'anda zaku Aura"Amma dai kinsan irin wannan Auren Ashara'ance bbu kyau ko? Hakane na sani"Amma ya zanyi dashi"yanamun barazanar idan ban Amince zaimun kaza da kaza"sai kuma tak**a kuka"kiyi hak'uri dan Allah kiyi shiru muyi mgn"da farko ban goyi bayansaba"Amma sbd wani dogon tunani danayi saina Amince"inaso ki shigo gidansa tsakani da Allah"ki zauna dashi bbu cuta bbu cutarwa"yanzun haka nazone sbd naga gidanku dan gobe nayima magabatansa jagoran zuwa nan"kuma kisanar Agida gobe insha Allah zai turo Ayi mgn"nasan kina k'alubalentar halayensa kina masa kallon marar kirki sbd matsalar da kuka samu kedashi Abaya"ba haka yakeba zancen gaskiya"Amma yanada murd'add'en halin daba kowa ke iya fahimtar saba"inaso na baki shawara game da yadda zaki zauna dashi"insha Allah zaki sami sauk'in zama dashi"Amma dole sai kinyi hak'uri"big man mutum ne meson agirmamashi"sannan karki sake ki shiga sabgarsa muddin bashine yasakokiba Aciki"sai Abu na k'arshe beson k'arya ,beson musu"sauren halayensa kuma ta hikimarki na y'a mace zaki canza manashi"jikina na bani Akwai abu me girma dazai faru tsakaninku nan gaba"inaso maganar nan ta tsaya daga ni saike"kuma idan Anyi Auren kowa zai zauna d'akinsa bbu ruwan wani da wani.... Ajiyar zuciya ummu tasaki sbd dama Abinda takeso tayi masa mgn kenan tanajin nauyi"kanta ak'asa tace"to ina Aiki na teaching"ina fatan zai barni naci gaba?"eh insha zaki dinga Aikin ki"sai zancen daya kawoni bayan zai turo shine yace"baya buk'atar kije da komai gidansa"daga ke sai kayanki na sawa zakije"yace"beson wata bidi'a"Amma na soke wannan dole mucashe Ana bikin big man"yafad'a cikin tsokana yana murmushi"kanta Ak'asa batace komaiba"zan wuce gida"saidai na manta bansanar miki wacece sa'ada ba"sa'ada k'anwarsa ce uwa d'aya uba d'aya"yanaji da ita sosai ina fatan kema zaki sota ki kula da ita sosai"insha Allah"to sufa wa'annan mazan guda biyu??"d'an murmushi yasaki yana dirowa dg samqn motar sbd yafahimci su tj take nufi"yana kallon ta yace"wad'annan y'an Abi yarima Asha kid'ane"wato k'ananun shaid'anune da suke tare dashi sbd dukiyarsa"kuma inaso insha Allah kiyi sanadin rabashi dasu...ni kuma Awa?"hmm ummulkhairy kenan"bazan b'oyemiki ba"wlh kunyi matuk'ar dacewa da big man"ina fatan wannan Auren yad'ore har Abada"yana fad'in hakan yabud'e k'ofar driver sit yashiga yana d'aga mata hannu"tsabar mamakin kalamansa kasa mgn ummu tayi ta juya jikinta Asanyaye ta nufi cikin gida"saidai tana ahiga soro ta k'ak'aro fara'ar dole sbd goggo Luba tasan tana cikin farin ciki"zama tayi tasanarwa mama gobe Abdallah zai turo magabatansa Ayi mgn"sosai maman tayi farin ciki"tana tunanin dole gobe Ayi shiri na musammun iya k'arfin su sbd kar Arainasu idan Anzo neman Auren.... goggo luba dake lab'e gefen window tanajin firan ummu da mama"bayan sun gama mgn ta wuce d'akinta da sauri da nufin ta koma gobe wajen boka....

Washe gari....✍️
Meson complete WhatsApp
0816 667 4823

Address

Kaduna
Zaria

Telephone

+2348166674823

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HAUSA NOVEL ONLY posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to HAUSA NOVEL ONLY:

Share